BindiddigiKo Gaskiya Ne Faransa Ta Maka Nijar A Kotun...

Ko Gaskiya Ne Faransa Ta Maka Nijar A Kotun Duniya Kan Uranium?

-

Tun bayan juyin mulki da akayi a kasar Nijar dai ake ta samun tataburza tsakanin kasar Faransa da Nijar wanda hakan ya haddasa yaduwar labarun karya.

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani ikirari  (archived here) ranar 22/12/2024 cewa “ 🛑Faransa ta maka Nijar kara kotun duniya saboda Uranium” wannan wallafa dai ta sami tofa albarkacin baki wato comments 350 da kuma shares 71, Sai kuma likes sama da dubu daya yayin wannan bincike.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta fara da bincikar batun alakar Faransa da Nijar kan Uranium inda ta gano cewa batun haka ko fitar da uranium daga Nijar ba gwamnatin Faransa bace face kamfani mai zaman kansa na Orano wanda yake amfani da wani kamfanin dake karkashin sa (subsidiary) mai suna Imouraren. Kasar ta Faransa dai nada hannun jari a kamfanin.
Sannan binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ta gano cewa kamfanin na Orano ya kai gwamnatin kasar ta Nijar sashen sulhu na kasa da kasa kan kwace lasisin aiki da kasa ta Nijar tayi.
Haka zalika da kafar bindiddigi ta Alkalanci y’a tuntubi ofishin jakadanci Faransa a Najeriya ya turowa da amsar cewa gwamnatin kasar Faransa bata kai Nijar kotu ba face kamfanin Orano ne ya kai kasar ta Nijar sashen sulhu wato arbitration a turance domin batun soke lasisin kamfanin dake karkarshin sa da gwamnatin Nijar tayi.

Sakamakon Bincike:

Bisa bayanan da kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta samu na tabbatar da cewa sashen sulhu aka kai kasar Nijar kuma ba gwamnatin kasar Faransa bace wato kamfanini Orano ne. Sannan kotun duniya na duba batun laifukan  yaki da wasu batutuwa na kasa da kasa  wanda yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar