BindiddigiShin An Haramta Jin Waƙoƙin Rarara A Nijar?

Shin An Haramta Jin Waƙoƙin Rarara A Nijar?

-

Dokokin ƙasar Nijar ga kafafen yaɗa labarai nada tsauri inda kafafen na gwamnati dama masu zaman kansu basa sanya waƙoƙin siyasa irin na Rarara.

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani rubutu (archived here) ranar 1/1/2025 inda yake cewa “An haramta sauraron waƙoƙin Rarara a Niger”
Wannan wallafa ta sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dari tara yayin haɗa wannan bincike.
Hoton Ikirarin Dake Cigaba Da Yaduwa.
Hoton Ikirarin Dake Cigaba Da Yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta tuntubi wani babban dan jarida dake babban birnin ƙasar ta Nijar Yamai mai suna Yusuf Abdoulaye inda ya bayyanawa Alkalanci cewa babu wata sanarwa makamanciyar hakan daga hukumomi.
Dama mu anan Nijar ba’a sanya waƙoƙin irin na Rarara a gidajen Rediyo domin dokokin gidajen yaɗa labarai nada tsauri. Tabbas akwai labarai dake yaɗuwa cewa Rarara yace zai yiwa Shugaba Tchiani waƙa ta ɓatanci. A hukumance gaskiya babu wancan labari kuma na tuntubi wasu jami’an gwamnati sunce ya zuwa yanzu (2/1/2025) babu wata sanarwa makamanciyar hakan.
Sannan kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntubi wani mamallakin gidan Radiyo a jihar Maraɗi Mansour Sani wanda yace ya zuwa ranar 2/1/2025 babu wata sanarwa a hukumance na wannan iƙirari zuwa ga gidajen Radiyo koma al’ummar gari, dama mu a gidajen Radiyo bama sanya waƙoƙin Rarara saboda na siyasa ne inji Mansour.
Tun bayan juyin mulkin soji a ƙasar ta Nijar dai babu ma’aikatar yaɗa labaru.

Sakamakon bincike:

Bisa la’akari da kasa samun wannan labari daga jami’an gwamnatin Nijar, sahihan gidajen jaridu da ƴan jaridun ƙasar, yasa kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan iƙirari ƙarya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar