BindiddigiKo Gaskiya Ne Faransa Ta Maka Nijar A Kotun...

Ko Gaskiya Ne Faransa Ta Maka Nijar A Kotun Duniya Kan Uranium?

-

Tun bayan juyin mulki da akayi a kasar Nijar dai ake ta samun tataburza tsakanin kasar Faransa da Nijar wanda hakan ya haddasa yaduwar labarun karya.

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani ikirari  (archived here) ranar 22/12/2024 cewa “ 🛑Faransa ta maka Nijar kara kotun duniya saboda Uranium” wannan wallafa dai ta sami tofa albarkacin baki wato comments 350 da kuma shares 71, Sai kuma likes sama da dubu daya yayin wannan bincike.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta fara da bincikar batun alakar Faransa da Nijar kan Uranium inda ta gano cewa batun haka ko fitar da uranium daga Nijar ba gwamnatin Faransa bace face kamfani mai zaman kansa na Orano wanda yake amfani da wani kamfanin dake karkashin sa (subsidiary) mai suna Imouraren. Kasar ta Faransa dai nada hannun jari a kamfanin.
Sannan binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ta gano cewa kamfanin na Orano ya kai gwamnatin kasar ta Nijar sashen sulhu na kasa da kasa kan kwace lasisin aiki da kasa ta Nijar tayi.
Haka zalika da kafar bindiddigi ta Alkalanci y’a tuntubi ofishin jakadanci Faransa a Najeriya ya turowa da amsar cewa gwamnatin kasar Faransa bata kai Nijar kotu ba face kamfanin Orano ne ya kai kasar ta Nijar sashen sulhu wato arbitration a turance domin batun soke lasisin kamfanin dake karkarshin sa da gwamnatin Nijar tayi.

Sakamakon Bincike:

Bisa bayanan da kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta samu na tabbatar da cewa sashen sulhu aka kai kasar Nijar kuma ba gwamnatin kasar Faransa bace wato kamfanini Orano ne. Sannan kotun duniya na duba batun laifukan  yaki da wasu batutuwa na kasa da kasa  wanda yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar