BindiddigiShin Nijar ta rabu da Faransanci?

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

-

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar ta bar harshen Faransanci.
To sai dai  ba kamar yadda wasu suka fahimci labarin ba ga yadda abin yake.
A yanzu dai kasar ta Nijar ta tabbatar da cewa Hausa ta zama harshen ƙasa wato langue nationale a Faransanci.

Wannan na nufin cewa harshen Hausa an amince shi a matsayin harshen da ke da muhimmanci wajen adana al’adu, sadarwa a tsakanin jama’a, da koyar da ilimi a matakin farko wato firamare amma hakan ba yana nufin baza’a koyar da yaren Faransanci ba. Haka zalika kasar ta bayyana wasu yaruka a kasar a matsayin masu muhimmanci.

Amfani da Hausa a matsayin harshen ƙasa yana nufin za a iya amfani da shi a:

Makarantun firamare.

Za’a dinga sadarwa da shirye-shirye a rediyo da Talabijin.

Tattaunawa tsakanin al’umma da hukumomi a matakin ƙasa.

Wayar da kan mutane kan wasu al’amuran da suka shafe su ko suka shafi kasa.

To amma inda gizo ke sakar shine harshen Faransanci har yanzu shine harshen aiki wato langues de travail a Faransanci.

Faransanci shine harshen da gwamnati za ta cigaba da amfani da shi wajen:
To amma fa baya ga Faransanci kasar ta kara da Turancin Ingilishi a matsayin harshen gwamnati.

sune dai za’a dinga;

Rubuce-rubuce a hukumance.

Takardun gwamnati da dokoki.

Tattaunawa da kasashen waje.

Zaman kotu da yanke hukunci a kotu.

Rubutu da karatu a jami’o’i da sauran manyan makarantu.

Kasar ta Nijar dai ba ta cire Faransanci a matsayin yaren gwamnati ba sai dai kara harshen turancin Ingilishi kamar yadda kasar Algeria tayi inda ake koyar da yara yarukan biyu a makarantu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar