BindiddigiKasashe KetareShin Nijar Ta Kori Jakadan Tarayyar Turai?

Shin Nijar Ta Kori Jakadan Tarayyar Turai?

-

Alakar kasar Nijar da kungiyoyin kasa da kasa dai ta fara samun matsala ne tun bayan juyin mulki, wanda aka dinga samun ikirari da labaran karya kan wasu matakan kasar ta Nijar dama su kungiyoyin.

Batu:

Wani shafin kafar sadarwa ta Facebook mai suna Damagaran Post ya wallafa wani ikirari na cewa (Adana bayanai a NAN) “kasar Nijar ta kori jakadan tarayyar turai daga kasar.”

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta fara da tuntubar kungiyar tarayya turai inda ta Sami sanarwar da tarayyar turan ta fitar a harshen Faransanci take cewa ta yiwa jakadan nata kiranye ne don jin bahasi.

Sanarwar tace; “Tarayyar turai dai ta sami sanarwar da gwamnatin Nijar ta fitar da take kalubalantar yadda wakilan tarayyar turai a kasar suka raba kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa. Tarayyar turai bata gamsu da zarge-zarge da rashin jituwar da gwamnatin Nijar take yiwa wakilan EU din ba. Wannan dalili yasa EU ta bukaci jakadanta dake Niamey daya je babban ofishin EU dake birnin Brussels domin jin bahasi.”
Ma’aikatar harkokin wajen Nijar dai na zargin EU da raba kayayyakin agaji ba tare da tuntuba ko sahalewar gwamnatin kasar ba.

To sai dai EU tace a yayin da kasar ta Nijar ke fama da matsaloli tana da kudirin cigaba da bada tallafi ga ‘yan kasar musamman ta amfani da hukumomin majalisar dinkin duniya dama kungiyoyin bada agaji na kasa da kasa.

Ma’aikatar harkokin wajen ta Nijar dai dama sun bukaci kungiyar ta EU data canza jakadan bisa zarginsa da yin katsalandan a harkokin cikin gidan kasar.

To sai dai EU ta musanta wancan zargi inda tace bazata bari a siyasantar da kayan agaji da take bayarwa ba.

Sakamakon Bincike:

Binciken kafar bindiddigi na Alkalanci dai ya rasa samo inda hukumomin kasar suka bukaci jakadan daya bar kasar wato sun koreshi fyace bukatar a canza musu shi. Wannan yasa wannan ikirari na Damagaram Post ya zama karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar