BindiddigiKasashe KetareShin Nijar Ta Kori Jakadan Tarayyar Turai?

Shin Nijar Ta Kori Jakadan Tarayyar Turai?

-

Alakar kasar Nijar da kungiyoyin kasa da kasa dai ta fara samun matsala ne tun bayan juyin mulki, wanda aka dinga samun ikirari da labaran karya kan wasu matakan kasar ta Nijar dama su kungiyoyin.

Batu:

Wani shafin kafar sadarwa ta Facebook mai suna Damagaran Post ya wallafa wani ikirari na cewa (Adana bayanai a NAN) “kasar Nijar ta kori jakadan tarayyar turai daga kasar.”

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta fara da tuntubar kungiyar tarayya turai inda ta Sami sanarwar da tarayyar turan ta fitar a harshen Faransanci take cewa ta yiwa jakadan nata kiranye ne don jin bahasi.

Sanarwar tace; “Tarayyar turai dai ta sami sanarwar da gwamnatin Nijar ta fitar da take kalubalantar yadda wakilan tarayyar turai a kasar suka raba kayan agaji ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa. Tarayyar turai bata gamsu da zarge-zarge da rashin jituwar da gwamnatin Nijar take yiwa wakilan EU din ba. Wannan dalili yasa EU ta bukaci jakadanta dake Niamey daya je babban ofishin EU dake birnin Brussels domin jin bahasi.”
Ma’aikatar harkokin wajen Nijar dai na zargin EU da raba kayayyakin agaji ba tare da tuntuba ko sahalewar gwamnatin kasar ba.

To sai dai EU tace a yayin da kasar ta Nijar ke fama da matsaloli tana da kudirin cigaba da bada tallafi ga ‘yan kasar musamman ta amfani da hukumomin majalisar dinkin duniya dama kungiyoyin bada agaji na kasa da kasa.

Ma’aikatar harkokin wajen ta Nijar dai dama sun bukaci kungiyar ta EU data canza jakadan bisa zarginsa da yin katsalandan a harkokin cikin gidan kasar.

To sai dai EU ta musanta wancan zargi inda tace bazata bari a siyasantar da kayan agaji da take bayarwa ba.

Sakamakon Bincike:

Binciken kafar bindiddigi na Alkalanci dai ya rasa samo inda hukumomin kasar suka bukaci jakadan daya bar kasar wato sun koreshi fyace bukatar a canza musu shi. Wannan yasa wannan ikirari na Damagaram Post ya zama karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar