BindiddigiShin Akwai Sansanin Sojan Faransa A jihar Borno?

Shin Akwai Sansanin Sojan Faransa A jihar Borno?

-

Gwamnatin kasar Nijar dai na cigaba da zargin gwamnatin Najeriya wajen cewa tana hada kai da kasar Faransa domin tada hargitsi a kasar ta Nijar. Wadannan zarge-zarge dai na zuwa da ikirarin karya.

Batu:

Akwai wani bidiyo dake yaduwa a kafofin sada zumunta da dama dake nuna shugaban mulkin soji na kasar Nijar yana hira da wani dan jarida inda a ciki yayi ikirarin cewa;
Shugaban Najeriya ya amshi kudi daga Faransa domin basu guri a Borno inda suka kafa wani sansanin soji gurin da suke kira “Canada”.

Bincike:

Binciken da kafar bindiddigi ta  Alkalanci  tayi tun kwanakin baya ya tabbatar da cewa babu sojin Faransa a jihar Borno balle ma kafa sansani.
Sabon bincike bayan wannan bidiyo wanda ya hada da tuntubar dakarun sojin Najeriya dake aiki a jihar Borno ya tabbatarwa da kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci cewa babu wani sojin Faransa dake yankunan Kurnawa, Kangarwa da Dogon Chikun da shugaban na Nijar yayi ikirari a bidiyon. Domin kuwa yanki ne da ‘yan kungiyar ISWAP ke kai farmaki sosai.
A kwanakin baya ma dai shalkwatar tsaron Najeriya ta musunta shirin kafa sansanin sojin wata kasa a Najeriya wanda aka dinga yada tsohon bidiyo sojin Birtaniya a matsayin sojin Faransa.
Mai magana da yawun ministan harkokin wajen Najeriya Alkasim Abdulkadir shima ya musunta samar da sansanin sojin Faransa mai suna CANADA a jihar ta Borno. “Tabbas shugaba Tinubu yaje Faransa wanda kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyoyi irin lafiya, sanya hannun jari, sufuri, noma da lantarki haka  kuma akwai ‘yan kasuwar Najeriya da suma suka sanya hannu domin fara bude kasuwancin su a Faransa . Najeriya kasace mai tasowa kuma ta sanya irin wannan yarjejeniya da kasashe irin su China, America, Rasha da Japan.
Ofishin jakadancin Faransa a Najeriya shima ya musunta shirin samar da sansanin soji a Najeriya.

Sakamakon bincike:

Bisa kasa samun wata hujja ta wanzuwar ko samuwar sansanin soji balle sojin wata kasa a yankin da shugaban na Nijar ya ambata yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar