BindiddigiShin Akwai Sansanin Sojan Faransa A jihar Borno?

Shin Akwai Sansanin Sojan Faransa A jihar Borno?

-

Gwamnatin kasar Nijar dai na cigaba da zargin gwamnatin Najeriya wajen cewa tana hada kai da kasar Faransa domin tada hargitsi a kasar ta Nijar. Wadannan zarge-zarge dai na zuwa da ikirarin karya.

Batu:

Akwai wani bidiyo dake yaduwa a kafofin sada zumunta da dama dake nuna shugaban mulkin soji na kasar Nijar yana hira da wani dan jarida inda a ciki yayi ikirarin cewa;
Shugaban Najeriya ya amshi kudi daga Faransa domin basu guri a Borno inda suka kafa wani sansanin soji gurin da suke kira “Canada”.

Bincike:

Binciken da kafar bindiddigi ta  Alkalanci  tayi tun kwanakin baya ya tabbatar da cewa babu sojin Faransa a jihar Borno balle ma kafa sansani.
Sabon bincike bayan wannan bidiyo wanda ya hada da tuntubar dakarun sojin Najeriya dake aiki a jihar Borno ya tabbatarwa da kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci cewa babu wani sojin Faransa dake yankunan Kurnawa, Kangarwa da Dogon Chikun da shugaban na Nijar yayi ikirari a bidiyon. Domin kuwa yanki ne da ‘yan kungiyar ISWAP ke kai farmaki sosai.
A kwanakin baya ma dai shalkwatar tsaron Najeriya ta musunta shirin kafa sansanin sojin wata kasa a Najeriya wanda aka dinga yada tsohon bidiyo sojin Birtaniya a matsayin sojin Faransa.
Mai magana da yawun ministan harkokin wajen Najeriya Alkasim Abdulkadir shima ya musunta samar da sansanin sojin Faransa mai suna CANADA a jihar ta Borno. “Tabbas shugaba Tinubu yaje Faransa wanda kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyoyi irin lafiya, sanya hannun jari, sufuri, noma da lantarki haka  kuma akwai ‘yan kasuwar Najeriya da suma suka sanya hannu domin fara bude kasuwancin su a Faransa . Najeriya kasace mai tasowa kuma ta sanya irin wannan yarjejeniya da kasashe irin su China, America, Rasha da Japan.
Ofishin jakadancin Faransa a Najeriya shima ya musunta shirin samar da sansanin soji a Najeriya.

Sakamakon bincike:

Bisa kasa samun wata hujja ta wanzuwar ko samuwar sansanin soji balle sojin wata kasa a yankin da shugaban na Nijar ya ambata yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar