BindiddigiKo Sojojin Faransa Sun Iso Najeriya?

Ko Sojojin Faransa Sun Iso Najeriya?

-

Kome yasa ake cigaba da yada labaran karya kan kasar Faransa a Najeriya bayan wasu kasashe sun bukaci sojojinsu su fice?

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Usman Yusuf Bala ya wallafa wani bidiyo dake nuna wani sojan Najeriya na magana kan yaki da ‘yan Boko Haram a gefensa akwai sojoji turawa wanda a saman bidiyon ya rubuta cewa “ Nan a France ne ko a Nigeria ne Sundai karaso kenan.”
Wannan bidiyo dai ya sami mutane sama da dubu goma sha uku da suka kalla a kasa da awanni 24 da wallafa shi.
Akwai dai ikirari da ake yadawa a harshen turanci na cewa sojojin Faransa sun iso Najeriya domin kafa sansani bayan korarsu wasu kasashe sukayi.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta dauki hoton wani sashe na bidiyo tare da binciken lokacin da aka dauka da kuma suwaye turawan?
Binciken ya nuna cewa turawan dake bidiyon na Ingila ne bana Faransa ba. Haka zalika baturen dake gefen sojin Najeriya ba wani bane face Kanal Martin Leach wanda sananne ne a tawagar horaswa ta sojin Birtaniya, ya kuma zama babban wanda ya karfafa alakar soji tsakanin sojojin Najeriya da Birtaniya.
Ko a watan Oktoban wannan shekara sojin da aka gani a bidiyon wato Kanal Leach ya kawowa Najeriya tallafin makaman yaki da suka kai kusan biliyan daya domin yaki da ‘yan Boko Haram.
Shalkwatar dakarun tsaro ta Operation Hadin kai itama ta musunta cewa akwai sojojin Faransa inda tace bidiyon da aka gani ba kowa bane face Birgediya Janar Haruna yake magana da ‘yan jaridu yayin da suka karbi tallafin makamai daga sojojin Burtaniya a watan Oktoba.

Sakamakon Bincike:

Kasancewar wannan bidiyo tsohon bidiyo ne kuma turawan da aka gani a bidiyon sojojin Burtaniya ne ba na Faransa ba kamar yadda ake ikirarin. Wannan yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari na cewa sojojin Faransa sun iso Najeriya karya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar