BindiddigiShin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali...

Shin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali Da Nijar Daga Watan Janairu?

-

Tun bayan juyin mulkin soji a kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar kasashen uku suka sami takun saka da kungiyar ECOWAS inda suka bayyana aniyar ficewa tare da hada wata kungiyar mai suna AES. Wannan abu yazo da labaran karya da ake yadawa a kafafen sada zamunta kan kasashen dama kungiyar ta ECOWAS.

Batu:

Wani shafin kafar sada zumunta ta Tiktok mai suna @bashthausa ya wallafa wani rubutu dake ikirarin cewa; “ECOWAS ta amince da Nijar, Mali da Burkina Faso daga cikinta.”
Rubuta ya kara da cewa ficewar ta kasashen zai fara daga watan Janairun shekarar 2025.

Bincike:

Binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ya sami sanarwar tare da saurarar bayanin bayan taron na shugabannin kasashen ECOWAS da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya inda shugaban ECOWAS Oumar Tourey ya sanar da kara wa’adin amincewa da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar zuwa wata shida daga 29 ga watan Janairun 2025, domin baiwa kasashen damar ganin sun janye matakin ficewa daga kungiyar ta ECOWAS.
Sanarwar ta bayyana cewa ranar 29 ga watan Janairun itace ranar ficewa a hukumance amma an dage ranar karshe ta zama ko ficewar kasashen zuwa 29 ga watan Yuli 2025, ECOWAS dai zatayi amfani da wannan lokaci domin ganin an sulhunta tsakanin kasashen da ECOWAS.
Kasashen na Burkina Faso, Mali da Nijar dai sunce babu jada baya kan ficewa daga ECOWAS amma yan kasashe mambobin ECOWAS zasu iya shiga kasashen ba tare da visa ba kamar yadda yake a yanzu.

Sakamakon Bincike:

Bisa sauraron jawabin shugaban kungiyar ECOWAS da umar kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin akwai kamshin gaskiya.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar