BindiddigiKasashen Turai Basu Ki Karbar Fasfo Din Kasashen AES...

Kasashen Turai Basu Ki Karbar Fasfo Din Kasashen AES Ba

-

Tun bayan juyin mulkin kasar Nijar labarun karya kala-kala ke yaduwa kan kasashe daban-daban wanda ya hada da Tarayyar Turai.

Ikirari:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram post ya wallafa wani ikirari a ranar 18/02/2025 inda yake cewa; “Sabon passport din AES ya kasa yin tasiri a tarayyar Turai yayin da ƙasashen Schengen suka ki karbar sa kuma suka hana visar Turai ga masu passport din.”

Bincike:

A farkon shekarar nan ne dai akai rawaito cewa kasar Burkina Faso ta kaddamar da fasfo din kasashen AES bayan ficewar su daga kungiyar ECOWAS.
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Nijar Amadou Ango Souley yace wannan ba gaskiya bane. “Wannan labarin karya ne kawai, babu magana irin wannan. Idan da akwai irin wanga magana da mun fitar da sako ga manema labarai. Suma da sun sanar damu.”
Sannan mun tuntubi Tarayyar Turai inda aka tabbatar mana da cewa wannan ikirari ba gaskiya bane. “Bada visa ayyukan ofishin jakadancin kasashen ne, kuma kowacce kasa tana da tsari da kuma abinda take dubawa kafin ta bada visa ko ta hana.

Sakamakon bincike:

Bisa bayanan ma’aikatar harkokin wajen Nijar da kuma jami’a daga kungiyar Tarayyar Turai na cewa babu wannan magana ta kin karbar fasfo din dake dauke da tambarin AES yasa kafar tantance labarai ta Alkalanci yanke hukuncin cewa karya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar