BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa...

Ina Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa Najeriya

-

Shekara da shekaru dai kasar Saudiyya na turowa Najeriya Dabino musamman gab da Azumin Ramadana a rabawa talakawa ko ‘yan gudun hijira.

Ikirari

Akwai wani bidiyo dake yawo a shafin sada zumunta na Tiktok mai suna @bello.galadanchi wanda aka wallafa a ranar 22/02/2025 inda wanda ke cikin bidiyon yayi ikirarin cewa dabino kadai Saudiyya ta turawa Najeriya bayan da ta sanya hannun jari na dala biliyan dari shida a kasar Amurka $600bn.

Bincike:

Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta gano cewa watan Disembar 2024 an bayyana cewa kasar Saudiyya ta sanya kudi a harkokin kasuwanci a Najeriya daya kai dala miliyan dubu daya da miliyan dari biyu $1.2bn.
Sannan a watan Janairun wannan shekarar ta 2025 kamfanin dillancin labaran kasar Saudiyya ya wallafa cewa kamfanonin kasar masu zaman kansu da jami’an gwamnatin Najeriya sun amince suyi aiki domin cigaba da zuba jari a Najeriya musamman a fannin ma’adanai, noma, kayan abinci, harkokin banki da fasaha.
A watan Nuwamban shekarar 2023 kasar ta Saudiyya da Najeriya suka amince da Saudiyya ta sanya hannun jari domin gyara matatun man Najeriya bayan da shugaba Tinubu ya ga na da Yariman Saudiyya Salman bn Yusuf.
Sannan kuma kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya kai Riyal miliyan dubu biyu da miliyan dari bakwai SAR 2.7bn.
Haka zalika kasar ta Saudiyya ta kashe kudi da ya ka dala miliyan arba’in da bakwai wajen bada agaji a garuruwa sama da 90 na Najeriya a cewar ofishin jakadancin kasar dake Najeriya.
Batun bada dabino dama dai kasar Saudiyya na ba wa kasashe dake da musulmai da yawa dabino duk lokacin azumi wanda ya hada da Najeriya. Idan za’a iya tunawa lokacin shugaban kasa Muhammadu Buhari sai da aka sami wata badakala kan boye dabino da akayi aka rabawa makusanta gwamnati maimakon’yan gudun hijira.

Sakamakon bincike:

Bisa lura da wadannan alkaluma wanda ya nuna cewa kasar Saudiyya ta sanya makuden kudade a Najeriya kuma ba dabino ka dai take aikowa Najeriya ba yasa kafar tantance labarai ta Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne. 
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar