BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa...

Ina Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa Najeriya

-

Shekara da shekaru dai kasar Saudiyya na turowa Najeriya Dabino musamman gab da Azumin Ramadana a rabawa talakawa ko ‘yan gudun hijira.

Ikirari

Akwai wani bidiyo dake yawo a shafin sada zumunta na Tiktok mai suna @bello.galadanchi wanda aka wallafa a ranar 22/02/2025 inda wanda ke cikin bidiyon yayi ikirarin cewa dabino kadai Saudiyya ta turawa Najeriya bayan da ta sanya hannun jari na dala biliyan dari shida a kasar Amurka $600bn.

Bincike:

Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta gano cewa watan Disembar 2024 an bayyana cewa kasar Saudiyya ta sanya kudi a harkokin kasuwanci a Najeriya daya kai dala miliyan dubu daya da miliyan dari biyu $1.2bn.
Sannan a watan Janairun wannan shekarar ta 2025 kamfanin dillancin labaran kasar Saudiyya ya wallafa cewa kamfanonin kasar masu zaman kansu da jami’an gwamnatin Najeriya sun amince suyi aiki domin cigaba da zuba jari a Najeriya musamman a fannin ma’adanai, noma, kayan abinci, harkokin banki da fasaha.
A watan Nuwamban shekarar 2023 kasar ta Saudiyya da Najeriya suka amince da Saudiyya ta sanya hannun jari domin gyara matatun man Najeriya bayan da shugaba Tinubu ya ga na da Yariman Saudiyya Salman bn Yusuf.
Sannan kuma kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya kai Riyal miliyan dubu biyu da miliyan dari bakwai SAR 2.7bn.
Haka zalika kasar ta Saudiyya ta kashe kudi da ya ka dala miliyan arba’in da bakwai wajen bada agaji a garuruwa sama da 90 na Najeriya a cewar ofishin jakadancin kasar dake Najeriya.
Batun bada dabino dama dai kasar Saudiyya na ba wa kasashe dake da musulmai da yawa dabino duk lokacin azumi wanda ya hada da Najeriya. Idan za’a iya tunawa lokacin shugaban kasa Muhammadu Buhari sai da aka sami wata badakala kan boye dabino da akayi aka rabawa makusanta gwamnati maimakon’yan gudun hijira.

Sakamakon bincike:

Bisa lura da wadannan alkaluma wanda ya nuna cewa kasar Saudiyya ta sanya makuden kudade a Najeriya kuma ba dabino ka dai take aikowa Najeriya ba yasa kafar tantance labarai ta Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne. 
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar