BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa...

Ina Gaskiyar Cewa Saudiyya Dabino Kadai Take Bai Wa Najeriya

-

Shekara da shekaru dai kasar Saudiyya na turowa Najeriya Dabino musamman gab da Azumin Ramadana a rabawa talakawa ko ‘yan gudun hijira.

Ikirari

Akwai wani bidiyo dake yawo a shafin sada zumunta na Tiktok mai suna @bello.galadanchi wanda aka wallafa a ranar 22/02/2025 inda wanda ke cikin bidiyon yayi ikirarin cewa dabino kadai Saudiyya ta turawa Najeriya bayan da ta sanya hannun jari na dala biliyan dari shida a kasar Amurka $600bn.

Bincike:

Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta gano cewa watan Disembar 2024 an bayyana cewa kasar Saudiyya ta sanya kudi a harkokin kasuwanci a Najeriya daya kai dala miliyan dubu daya da miliyan dari biyu $1.2bn.
Sannan a watan Janairun wannan shekarar ta 2025 kamfanin dillancin labaran kasar Saudiyya ya wallafa cewa kamfanonin kasar masu zaman kansu da jami’an gwamnatin Najeriya sun amince suyi aiki domin cigaba da zuba jari a Najeriya musamman a fannin ma’adanai, noma, kayan abinci, harkokin banki da fasaha.
A watan Nuwamban shekarar 2023 kasar ta Saudiyya da Najeriya suka amince da Saudiyya ta sanya hannun jari domin gyara matatun man Najeriya bayan da shugaba Tinubu ya ga na da Yariman Saudiyya Salman bn Yusuf.
Sannan kuma kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya kai Riyal miliyan dubu biyu da miliyan dari bakwai SAR 2.7bn.
Haka zalika kasar ta Saudiyya ta kashe kudi da ya ka dala miliyan arba’in da bakwai wajen bada agaji a garuruwa sama da 90 na Najeriya a cewar ofishin jakadancin kasar dake Najeriya.
Batun bada dabino dama dai kasar Saudiyya na ba wa kasashe dake da musulmai da yawa dabino duk lokacin azumi wanda ya hada da Najeriya. Idan za’a iya tunawa lokacin shugaban kasa Muhammadu Buhari sai da aka sami wata badakala kan boye dabino da akayi aka rabawa makusanta gwamnati maimakon’yan gudun hijira.

Sakamakon bincike:

Bisa lura da wadannan alkaluma wanda ya nuna cewa kasar Saudiyya ta sanya makuden kudade a Najeriya kuma ba dabino ka dai take aikowa Najeriya ba yasa kafar tantance labarai ta Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne. 
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar