BindiddigiShin Dangote Yace Litar Man Fetur Zata Koma N500?

Shin Dangote Yace Litar Man Fetur Zata Koma N500?

-

Tun bayan samun saukin farashin man fetur daga matatar man Dangote dama kamfanin NNPCL ake samun labarai iri-iri harda na ƙarya.

Batu:

Wani shafin Facebook mai suna Taskira – H Online Tv ya wallafa wani iƙirari (archived here) a ranar 4/1/2025 inda yace; “YANZU YANZU: litar Man fetur zata koma Naira (500) nan Nada jimawa Ba, Dangote.”
Hoton iƙirarin ƙarya dake cigaba da yaduwa.
Hoton iƙirarin ƙarya dake cigaba da yaduwa.
Wani shafin Facebook mai suna Wakiliya a ranar (archived here) 3/1/2025 ya wallafa cewa “YANZU YANZU: litar Man fetur zata koma Naira (500) nan Nada jimawa Ba, Dangote.”
Hoton iƙirarin ƙarya dake cigaba da yaduwa.
Hoton iƙirarin ƙarya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta tuntubi mai magana da yawun rukunin kamfanin Dangote Anthony Chiejina inda yace “wannan labari karya ne. Tabbas mun fitar da sanarwar sanya hannu kan yarjejeniya da kamfanoni kan man fetur, amma cewa munce farashin man fetur zai koma Naira dari biyar nan bada dadewa ba, karya ne.”
Haka zalika kafar bindiddigi ta Alkalanci ta duba kafafen yada labarai bata samu wannan labari ba a sahihan gidajen jaridu.

Sakamakon bincike:

La’akari da bayanin mai magana da yawun rukunin kamfanin Dangote daya karyata wannan labari, da kuma kasa samun wata sahihiyar kafar yada labarai data rawaito wannan labari, yasa kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan iƙirari ƙarya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar