BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Bappa Bichi Ya Ziyarci Shekarau?

Ina Gaskiyar Cewa Bappa Bichi Ya Ziyarci Shekarau?

-

Yayin da gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yiwa majalisar zartarwar jihar garambawul tare da korar wasu ‘yan majalisar zartarwa wanda ya hada da sakataren gwamnatin jihar Bappa Bichi an sami labaran karya da mutane ke yadawa wanda ya hada harda wasu gidajen radiyo a jihar.

Batu:

Wani shafi mai suna Daily Post ya wallafa labarin cewa “Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano Ya Ziyarci Shekaru”.
Sannan wani shafin Facebook mai suna Ammasco Radio yayi ikirarin cewa tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Abdullahi Bappa Bichi ya kaiwa tsohon gwamnan jihar Kano Ibrahim shekarau ziyara.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntubi Sule Ya’u Sule mai magana da yawun tsohon gwamnan jihar Kano Malam Ibrahim Shekaru inda ya fadawa Alkalanci cewa “hoton da ake yadawa tsohon hotone lokacin da shi Bappa Bichi ya kaiwa Shekarau jaje yayin da akai gobara a gidansa.” Ya kara da cewa “Idan akwai wani abu kamar haka (ganawa) tabbas bazai tafi ba tare da an sani ba.”
Haka zalika Alkalanci ta tuntubi bangaren Bappa Bichi inda makusantansa suka bayyana cewa hoton da ake yadawa tsohon hotone kuma tsohon sakataren gwamnatin bai ziyarci tsohon gwamnan ba.

Sakamakon Bincike:

Bisa samun tabbacin cewa hoton da ake yadawa tsoho ne kuma masu magana da yawun Bappa Bichi da Ibrahim Shekaru sun karyata faruwar ganawa tsakanin mutanen biyu tun bayan korar Bappa Bichi. Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar