BindiddigiShin Gwamnan Ribas Ya Haramta Ayyukan NNPC A Jihar?

Shin Gwamnan Ribas Ya Haramta Ayyukan NNPC A Jihar?

-

A ranar larabe ce dai wata kotun tarayya a Abuja ta baiwa babban bankin kasar CBN da ofishin akanta janar na kasar da kada su baiwa gwamna jihar Ribas kudin wata a ake baiwa jihohi.

Batu:

Wani labari dai yana yadu matuka a harshen turanci wanda wasu suka fara fassarashi zuwa Hausa Ina labarin ke cewa “Gwamnan jihar Ribas Sim Fubura ya rufe kamfanin NNPC da duk kamfanonin hakar mai a jihar inda ya ayyana cewa Idan akace babu kudin jihar daga gwamnatin tarayya to babu hakar mai…”
Labarin ya kara da cewa “…Mintuna kadan da wannan ayyanawa Najeriya ta sauka daga matsayin kasa ta hudu mai hako mai zuwa kasa ta ashirin da hudu.
Wani mai suna Manir Ahmad a shafinsa na Facebook ya wallafa wannan labari inda yake cewa “Alaji Fubara ya tsaya da kafafuwan sa fa.”
Sannan an sami wasu da suka yada irin wannan labari da salo daban-daban.
Bincike:
Binciken Alkalanci ya gano ya tuntubi kwamishinan yada labaran jihar Warisenibo Johnson inda yace labarin karya ne, gwamnatin Ribas mai mutunta doka ce.
Sannan binciken Alkalanci ya gano cewa Najeriya ba itace kasa ta hudu dake samar Ko fitar da man fetur ba,balle har ta sauka daga wannan mataki. rahoton hukumar makamashi na duniya wato IEA ya nuna cewa a bangaren samar da danyen mai Najeriya ce kasa ta 2 a Afrika a shekarar 2022.
Yayin da ta zama kasa ta goma sha shida a duniya.

Sakamakon Bincike:

Bisa wannan bincike Alkalanci ya yanke hukuncin cewa wannan labari karya ne wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar