BindiddigiKo Majalisar Dinkin Duniya Na Neman Masu Fassara A...

Ko Majalisar Dinkin Duniya Na Neman Masu Fassara A Jihohin Arewacin Najeriya?

-

Yaren Hausa dai na cikin yarukan dake kara samun tagomashi a kasashen duniya dama kungiyoyin kasa-da-kasa domin kokarin isar da sako ga miliyoyin masu magana da Yaren a yammaci da tsakiyar Afrika.

Batu:

A ‘yan satittikan da suka gabata dama zuwa yanzu an sami mutane da dama dake yada wani rubutu da aka wallafa dake dauke da hoton hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijira Ta Majalisar Dinkin Duniya UNHRC inda sanarwar ke cewa UN na neman masu fassara daga wasu jihohin arewacin Najeriya.
An dai ta yada wannan rubutu a WhatsApp dama sauran kafofin sada zumunta wanda ya hada da Facebook.
Misali akwai wani mai suna Muhammad Nafiu wanda ya wallafa wannan sanarwa a shafinsa na Facebook.
Akwai wani shafi mai suna www.ngojobsite.com ya wallafa wannan sanarwa a ranar 14 ga watan Oktaban 2024 na bukatar masu fassara.
Jihohin da sanarwar tace ana neman masu Fassarar sun hada da Adamawa, Borno, Gombe, Jagawa, Kaduna, Kano, sauran sune Katsina, Kebbi, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara.
A karshen sakon dake wannan shafi ya nuna cewa duk wanda yake da sha’awar aikin zai tura sakon e-mail zuwa ga wani e-mail da aka rubuta kamar haka (Interested and qualified candidates should send their Applications to: [email protected] using the job title as the subject of the mail.)

Bincike:

Alkalanci ta tuntubi maimagana da yawun hukumar ta UNHCR a Najeriya Gabriel Adeyemi inda ya bayyana cewa “Banga wannan sanarwa ba kuma banda labarinta, ina mai tabbatar maka duk sanarwa musamman ta daukar aiki indai baya shafin hukumar to karya ne.”
Sannan mun tuntubi mani jami’i a ofishin majalisar dinkin duniya shima ya yace baida masaniya dangane da batun daukar masu fassara tare da karin cewa UN na wallafa bukatar daukar ma’aikata a shafinta dama jaridu Idan bukatar hakan ta taso.

 

Sakamakon bincike:

Bisa bayanan mai magana da yawun hukumar ta UNHCR a Najeriya dama duba shafin UNHCR da UN, haka zalika da bayanin wani ma’aikacin ofishin majalisar dinkin duniya a Najeriya da Alkalanci ya tattaro ya tabbatar da cewa wannan sanarwa karya ce wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar