Yaren Hausa dai na cikin yarukan dake kara samun tagomashi a kasashen duniya dama kungiyoyin kasa-da-kasa domin kokarin isar da sako ga miliyoyin masu magana da Yaren a yammaci da tsakiyar Afrika.
Batu:
A ‘yan satittikan da suka gabata dama zuwa yanzu an sami mutane da dama dake yada wani rubutu da aka wallafa dake dauke da hoton hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijira Ta Majalisar Dinkin Duniya UNHRC inda sanarwar ke cewa UN na neman masu fassara daga wasu jihohin arewacin Najeriya.
An dai ta yada wannan rubutu a WhatsApp dama sauran kafofin sada zumunta wanda ya hada da Facebook.
Misali akwai wani mai suna Muhammad Nafiu wanda ya wallafa wannan sanarwa a shafinsa na Facebook.

Akwai wani shafi mai suna www.ngojobsite.com ya wallafa wannan sanarwa a ranar 14 ga watan Oktaban 2024 na bukatar masu fassara.

Jihohin da sanarwar tace ana neman masu Fassarar sun hada da Adamawa, Borno, Gombe, Jagawa, Kaduna, Kano, sauran sune Katsina, Kebbi, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara.
A karshen sakon dake wannan shafi ya nuna cewa duk wanda yake da sha’awar aikin zai tura sakon e-mail zuwa ga wani e-mail da aka rubuta kamar haka (Interested and qualified candidates should send their Applications to: [email protected] using the job title as the subject of the mail.)
Bincike:
Alkalanci ta tuntubi maimagana da yawun hukumar ta UNHCR a Najeriya Gabriel Adeyemi inda ya bayyana cewa “Banga wannan sanarwa ba kuma banda labarinta, ina mai tabbatar maka duk sanarwa musamman ta daukar aiki indai baya shafin hukumar to karya ne.”
Sannan mun tuntubi mani jami’i a ofishin majalisar dinkin duniya shima ya yace baida masaniya dangane da batun daukar masu fassara tare da karin cewa UN na wallafa bukatar daukar ma’aikata a shafinta dama jaridu Idan bukatar hakan ta taso.
Sakamakon bincike:
Bisa bayanan mai magana da yawun hukumar ta UNHCR a Najeriya dama duba shafin UNHCR da UN, haka zalika da bayanin wani ma’aikacin ofishin majalisar dinkin duniya a Najeriya da Alkalanci ya tattaro ya tabbatar da cewa wannan sanarwa karya ce wato false a turance.