Hukunci: Ƙarya ne
Bisa kasa samun wannan labari a shafukan shugaban ƙasa Tinubu, da sauran sahihan gidajen jaridu, tare da gano cewa lokaci na ƙarshe da Tinubu ya ambaci sunan tsohon shugaban ƙasa marigayi Yar'adua shine a watan Mayun shekarar 2023. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin cewa; Tinubu yace ya kamata iyalan Yar'adua su fi kowane mutum a Najeriya jin daɗi, hakan yasa na basu bashin billion 5 Naira sai nan da shekara ɗari su biya" Ƙarya ne.
Akwai wani iƙirari dake yaɗuwa matuƙa a shafukan sada zumunta dangane da iyalan tsohon shugaban ƙasar Najeriya marigayi Umaru Musa Yar’adua.
Iƙirari:
Wani shafin Tiktok mai suna Malam Khan ya wallafa wani iƙirari dake cewa; “Tinubu yace ya kamata iyalan Yar’adua su fi kowane mutum a Najeriya jin daɗi, hakan yasa na basu bashin billion 5 Naira sai nan da shekara ɗari su biya.”
Wanna wallafa ta sami mutane da dama da suka tofa albarkacin baki tare da kara wallafa ta.

Bincike:
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta fara da duba shafukan sada zumuntar shugaban ƙasa Bola Tinubu don ganin wannan labari amma babu wani abu makamancin hakan. Binciken Alkalanci ya gano cewa lokaci na ƙarshe da Tinubu ya ambaci sunan tsohon shugaban ƙasar Najeriya marigayi Umaru Musa Yar’adua shine a watan Mayun shekarar 2023.
Kuma a wancan lokaci yana magana ne kan tunawa da marigayin tare da alkawarin yin shugaban ci irin nashi, hakan ya faru ne kafin a rantsar dashi Tinubu.
Alkalanci ta ƙara da bincika ko akwai wata sahihiyar kafar yaɗa labarai data rawaito wannan labari amma babu, duk da girman sa.
Sannan kafar tantance labarai ta Alkalanci ta aika sakon tuntuɓa don jin inda mai shafin Tiktok ɗin don jin inda ya samo labarin to amma bayan ya karanta sama da awanni kusan 24 bai amsa ba.

Mun ajiye wannan ikirari wanda zaku iya gani koda wanda ya wallafa ya goge a nan.
Sakamakon bincike:
Bisa kasa samun wannan labari a shafukan shugaban ƙasa Tinubu, da sauran sahihan gidajen jaridu, tare da gano cewa lokaci na ƙarshe da Tinubu ya ambaci sunan tsohon shugaban ƙasa marigayi Yar’adua shine a watan Mayun shekarar 2023. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin cewa; Tinubu yace ya kamata iyalan Yar’adua su fi kowane mutum a Najeriya jin daɗi, hakan yasa na basu bashin billion 5 Naira sai nan da shekara ɗari su biya” Ƙarya ne.
