Fayyace abubuwaWa za a iya kira matashi a hukumance?

Wa za a iya kira matashi a hukumance?

-

A ranar 12 ga watan Agusta ne dai aka gudanar da ranar matasa ta duniya.

Batun ko wa za a iya kira matashi dai ya sha ban-ban tsakanin kasashen duniya.
Majalisar dinkin ta sanya wanda za’a iya kira matashi shine daga dan shekara 15 zuwa 24.
Itama hukumar lafiya ta majalisar dinkin duniya WHO ta bayyana wanda za’a iya kira matashi shine wanda yake tsakanin shekaru 15 zuwa 24.
To amma Asusun kula da yara na majalisar dinkin duniya UNICEF ya ce matashi shine dan shekaru 14 zuwa 29.
A Turai kuma matashi shine dan shekaru 14 zuwa 24 to amma kuma matasa sune ‘yan shekaru 14 zuwa 29 a wasu lokutan kuma yana kai har yan shekaru 35.
Idan muka dawo Najeriya kuma a hukumance matashi shine dan shekaru 15 zuwa 29 bayan da gwamnatin kasar ta sauya daga tsohon tsari a shekarar 2019 wanda a baya Najeriya na ganin matashi shine dan shekaru 18 zuwa 35.
Kasashen Afrika da dama dai na daukar matashi shine dan shekaru 18 zuwa 35.
A yanzu haka duk wanda yayin kammala jami’a ya kasance ya haura shekaru 30 bazai yi hidimar kasa ba wato NYSC. Wannan na cikin abinda ke nuna ko waye matashi a hukumance a Najeriya.
To duk da wannan sauyi a Najeriya kungiyoyin matasa na NYCN, majalisar dokokin matasa wato Youth parliament da sauransu masu jagorancin sun haura  shekaru 30 wasu ma sun kai kusan 40.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar