Fayyace abubuwaWaɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin...

Waɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin ƴan tawaye a Sudan?

-

Ayyana gwamnatin ƴan tawaye da jagoran RSF Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya yi a Sudan, ya zo a daidai lokacin da yaƙin basasar ƙasar ke cika shekara biyu, wanda ke nuna cewa yanzu kasar ta rabu gida biyu.

Ƙasashe da ake ganin suna goyon baya da kuma tattaunawa da gwamnatin ƴan adawa ta RSF sun hada da, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa UAE da Kenya da Chadi da Sudan ta Kudu da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka da Habasha da kuma Uganda. Akwai kuma wani ɓangare na Sojojin Libya da suka ɓalle.

A lokacin da yake ayyana kafa gwamnatin adawa a ranar 15 ga watan Afrilu wannan shekarar, Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya godewa Habasha da Chadi da Uganda da kuma Kenya. Birnin Nyala na yankin Darfur ne zai zama  fadar gwamnatin ta RSF da kungiyoyin kawance. Yawancin ƙungiyoyi da ke riƙe da makamai da kuma na siyasa sun yi yarjejeniya da RSF a watan Fabrairun bana, kan kafa gwamnatin da za ta fito daga yankunan Darfur da Kurdufan.

A watan Fabrairu, Al-Hadi Idris Yahya, babban jigon ƙungiyar Tasses ya yi iƙirarin cewa “suna da yakinin za su samu goyon baya daga ƙasashe da dama” kan kafa gwamnatin.

Ayyana gwamnatin ya ƙara janyo rarrabuwar kawuna a Sudan da kuma saka fargabar cewa ƙasar za ta faɗa cikin mawuyacin hali la’akari da halin gwamnatoci biyu da ake dasu a Libya.

RSF da ƙawancen ƙungiyoyi sun bayyana shirin fito da “sabuwar takardar kuɗi da kuma takardun zama ɗan ƙasa”, wanda masana ke ganin yunkurin ɓallewa ne.

Sai dai, Dagalo ya yi watsi da zargin neman ɓallewa daga Sudan. A maimakon haka, ya zargi gwamnatin sojin ƙasar da yin wasu abubuwa da za su kai ga rabewa, da kuma dawo da irin kuskuren da ya janyo ballewar Sudan ta Kudu.

Gwamnatin ƴan adawar za ta samar da sojoji da kuma ƴan sanda iri ɗaya, yayin da RSF da ƙungiyoyin ƙawance na ƴan bindiga za su kasance jigon dakarun.

Majalisar Ɗinkin Duniya, Ƙungiyar Tarayyar Afrika AU, Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa da Tarayyar Turai EU da kuma Amurka sun nuna adawa  da batun kafa gwamnatin ƴan tawaye da kuma nuna goyon baya ga haɗin-kan Sudan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar