Fayyace abubuwaWaɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin...

Waɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin ƴan tawaye a Sudan?

-

Ayyana gwamnatin ƴan tawaye da jagoran RSF Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya yi a Sudan, ya zo a daidai lokacin da yaƙin basasar ƙasar ke cika shekara biyu, wanda ke nuna cewa yanzu kasar ta rabu gida biyu.

Ƙasashe da ake ganin suna goyon baya da kuma tattaunawa da gwamnatin ƴan adawa ta RSF sun hada da, Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa UAE da Kenya da Chadi da Sudan ta Kudu da Jamhuriyar Tsakiyar Afirka da Habasha da kuma Uganda. Akwai kuma wani ɓangare na Sojojin Libya da suka ɓalle.

A lokacin da yake ayyana kafa gwamnatin adawa a ranar 15 ga watan Afrilu wannan shekarar, Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya godewa Habasha da Chadi da Uganda da kuma Kenya. Birnin Nyala na yankin Darfur ne zai zama  fadar gwamnatin ta RSF da kungiyoyin kawance. Yawancin ƙungiyoyi da ke riƙe da makamai da kuma na siyasa sun yi yarjejeniya da RSF a watan Fabrairun bana, kan kafa gwamnatin da za ta fito daga yankunan Darfur da Kurdufan.

A watan Fabrairu, Al-Hadi Idris Yahya, babban jigon ƙungiyar Tasses ya yi iƙirarin cewa “suna da yakinin za su samu goyon baya daga ƙasashe da dama” kan kafa gwamnatin.

Ayyana gwamnatin ya ƙara janyo rarrabuwar kawuna a Sudan da kuma saka fargabar cewa ƙasar za ta faɗa cikin mawuyacin hali la’akari da halin gwamnatoci biyu da ake dasu a Libya.

RSF da ƙawancen ƙungiyoyi sun bayyana shirin fito da “sabuwar takardar kuɗi da kuma takardun zama ɗan ƙasa”, wanda masana ke ganin yunkurin ɓallewa ne.

Sai dai, Dagalo ya yi watsi da zargin neman ɓallewa daga Sudan. A maimakon haka, ya zargi gwamnatin sojin ƙasar da yin wasu abubuwa da za su kai ga rabewa, da kuma dawo da irin kuskuren da ya janyo ballewar Sudan ta Kudu.

Gwamnatin ƴan adawar za ta samar da sojoji da kuma ƴan sanda iri ɗaya, yayin da RSF da ƙungiyoyin ƙawance na ƴan bindiga za su kasance jigon dakarun.

Majalisar Ɗinkin Duniya, Ƙungiyar Tarayyar Afrika AU, Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa da Tarayyar Turai EU da kuma Amurka sun nuna adawa  da batun kafa gwamnatin ƴan tawaye da kuma nuna goyon baya ga haɗin-kan Sudan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar