BindiddigiShin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya...

Shin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya gyara Najeriya cikin shakara daya?

-

Gabatarwa

Shekaru da dama dai yan Najeriya na ganin cewa kasar bata kan turbar dai-dai wato tana bukatar saiti ko ace gyara, musamman yadda ake fito da yadda aka sami wasu da suka rike shugabanci da almundahan tare da yin rub-da-ciki da kudaden yan kasar.

Wasu kasashe dai musamman a Asiya nada tsarin hukunci mai tsauri ga duk shugaban da aka samu da cin hanci Ko rashawa. Kasar Koriya ta arewa na cikin kasashen da mutane ke ganin cewa shugaban kasar baya wasa da batun doka da oda da kuma tabbatar da kasar ta sami cigaba da fannin mallakar makamai wanda ya hada da makamin kare dangi na nuclear.

Ikirari

Wani shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa ya wallafa wani rubutu tare da hoton shugaban kasar Korea ta arewa inda rubutun ke cewa;
“Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal. Kuma idan aka ba ni Nijeriya na yi masu mulkin mallaka, a cikin shekara daya zan mayar da su cikin rukunin manyan kasashen duniya, Cewar matashin Shugaban Kasar Koriya ta Arewa Kin Jong Un. Me za ku ce?”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Wannan rubutu ya sami yadawa wato shares sama da dari uku yayin da mutane da dama suka bayyana nasu ra’ayin.
Misali Yusuf Musa Numan yace “Ni nasan da hakan zai kasance tabbas zaka iya gyara Najeriya.”

A shafin X wato Twitter wata mai lakabin @Ameenatu_ itama ta wallafa irin wancan post inda yake cewa; “Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal-Inji shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un.”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Mutane sama da dari biyu ne suka tofa albarkacin bakinsu yayin da mutane sama da dadi bakwai suka danna like.
Bincike

An taba wallafa makamancin wannan kalamai a shekarar 2018 wanda Binciken da kafar jarida ta ICIR tayi ya nuna cewa wani shafi mai yada labaran karya da farfaganda mai suna Aljazeera West Africa ce ta fara wallafa shi. Saboda rashin shaida za’a iya cewa wancan labarin na aka sabunta ya dawo domin cimma wata manufa.

Sakamakon Bincike

Bincike da alkalanci yayi ya nuna cewa wannan bayani karya ne kawai, wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar