BindiddigiShin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya...

Shin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya gyara Najeriya cikin shakara daya?

-

Gabatarwa

Shekaru da dama dai yan Najeriya na ganin cewa kasar bata kan turbar dai-dai wato tana bukatar saiti ko ace gyara, musamman yadda ake fito da yadda aka sami wasu da suka rike shugabanci da almundahan tare da yin rub-da-ciki da kudaden yan kasar.

Wasu kasashe dai musamman a Asiya nada tsarin hukunci mai tsauri ga duk shugaban da aka samu da cin hanci Ko rashawa. Kasar Koriya ta arewa na cikin kasashen da mutane ke ganin cewa shugaban kasar baya wasa da batun doka da oda da kuma tabbatar da kasar ta sami cigaba da fannin mallakar makamai wanda ya hada da makamin kare dangi na nuclear.

Ikirari

Wani shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa ya wallafa wani rubutu tare da hoton shugaban kasar Korea ta arewa inda rubutun ke cewa;
“Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal. Kuma idan aka ba ni Nijeriya na yi masu mulkin mallaka, a cikin shekara daya zan mayar da su cikin rukunin manyan kasashen duniya, Cewar matashin Shugaban Kasar Koriya ta Arewa Kin Jong Un. Me za ku ce?”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Wannan rubutu ya sami yadawa wato shares sama da dari uku yayin da mutane da dama suka bayyana nasu ra’ayin.
Misali Yusuf Musa Numan yace “Ni nasan da hakan zai kasance tabbas zaka iya gyara Najeriya.”

A shafin X wato Twitter wata mai lakabin @Ameenatu_ itama ta wallafa irin wancan post inda yake cewa; “Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal-Inji shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un.”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Mutane sama da dari biyu ne suka tofa albarkacin bakinsu yayin da mutane sama da dadi bakwai suka danna like.
Bincike

An taba wallafa makamancin wannan kalamai a shekarar 2018 wanda Binciken da kafar jarida ta ICIR tayi ya nuna cewa wani shafi mai yada labaran karya da farfaganda mai suna Aljazeera West Africa ce ta fara wallafa shi. Saboda rashin shaida za’a iya cewa wancan labarin na aka sabunta ya dawo domin cimma wata manufa.

Sakamakon Bincike

Bincike da alkalanci yayi ya nuna cewa wannan bayani karya ne kawai, wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar