Fayyace abubuwaShin gwamnatin jiha nada hurumin rufe gidan radiyo?

Shin gwamnatin jiha nada hurumin rufe gidan radiyo?

-

Gwamnan jihar Neja dake arewa maso tsakiyar Najeriya ya  bayar da umarnin rufe tare kwace lasisin gidan radiyo mai suna Badeggi FM, saboda zargin Ingiza mutane su tada tarzoma wanda gidan radiyon ya musanta.

Wa zai iya rufe gidan radiyo?
Kundin tsarin mulkin Najeriya sashe na 39 ya baiwa ‘yan kasa damar mallaka tare da bude gidan jarida…
Dokar Najeriya dai ta baiwa hukumar kula da kafafen yada labarai NBC damar cin tara, soke lasisi tare da rufe kafar yada labarai Idan har an sami kafar da laifi bayan bincike.
Shugaban kungiyar lauyoyi ta Najeriya Afam Osigwe ya ce “babu wanda doka ta bashi damar rufe gidan jarida ba tare da bin doka ba.”
Itama ma’aikatar yada labarai ta Najeriya a wata sanarwar manema labarai da mai baiwa ministan yada labarai shawar Rabi’u Ibrahim ya sanyawa hannu ta tabbatar da cewa hurumin rufe ko soke lasisin gidan jarida na karkashin hukumar kula da kafafen yada labarai ta Najeriya wato NBC ce kawai.
Gwamnatin tarayya ta bukaci gwamnatin jihar ta Neja da ta mika korafinta kan gidan jaridar ga hukumar NBC.
Sakamakon bincike:
Bisa bayanin kundun tsarin mulkin Najeriya, kungiyar lauyoyi ta kasa da kuma ma’aikatar yada labarai ta Najeriya suka tabbatar da cewa hurumin dakatar ko soke lasisin gidan jarida na hannun hukumar NBC ne ba wata hukuma ko gwamnatin jiha ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar