BindiddigiShin Gaskiyane Mali Ta Fita Daga Kangin Bashin Kasashen...

Shin Gaskiyane Mali Ta Fita Daga Kangin Bashin Kasashen Waje?

-

Hausawa sukace bashi hanji ne… wato yana cikin kowa- Kasashen Afirka na cikin kasashen duniya dake karbar basussuka daga bankunan kasa da kasa dama kasashe kansu.

Batu:

Wani shafi mai suna Daily News Hausa 24 ya wallafa cewa; “ A daidai lokacin da Nigeria ke kara ciyo dinbin bashi daga kasashen waje, sai gashi  Yanzu haka ƙasar Mali babu kasar da ke binta bashi duk duniya.
Yaushe kuke ganin Nigeria za ta gama biyan bashin da ake bin ta ?”
Wasu shafuka sun wallafa irin wannan rubutu kuma ya sami shares da dama.

Bincike:

Alkalanci yayi bincike kan wannan ikirari inda muka fara da duba kome asusun bada lamuni na IMF ke cewa Kan bashin da ake bin kasar Malin.
Mun gano cewa ya zuwa shekarar 2022 bashin kasashen waje dake kan kasar Mali ya haura dala biliyan shida ($6,342,843,423)) a bara dai asusun bada lamunin na IMF ya nuna damuwa kan yadda Mali ke samun karuwar basussuka.
Sannan mun duba shafin bankin duniya inda muka samo jerin bankuna dama kasashen dake bin kasar Mali bashin wanda ya hada da bankin duniya, bankin bunkasa Afrika, bankin bunkasa yammacin Afrika, gwamnatin Faransa, Chana, Indiya, Abu Dhabi. Kuma kashi 30 na bashin daga kasashen wajen a kudin Euro ne a cewar rahoton bankin duniya.
Bamu tsaya anan ba mun bincika me ita gwamnatin Mali ke cewa Kan basussuka, sai muka samo bayanin ministan tattalin arzikin kasar Alousseni Sanou inda yace kasar na kokarin biyan bashin cikin gida daya kai dala miliyan dari uku da talatin da uku ($332 million).
Sannan bankin bunkasa nahiyar Afrika ya fitar da jerin kasashen da bashinsu bashi da yawa wanda kasar ta Mali bata ciki.

 

Sakamakon Bincike:

Bisa wadannan alkaluma da bincike da Alkalanci yayi inda ya kasa samo sahihan labari Ko ikirari dake nuna cewa kasar ta Mali ta zama kasar da ba’a binta  bashi ya nuna cewa wannan labari karya ne domin kuwa babu wata kafar yada labarai sananniya a Afrika Ko a wajen Afrika data rawaito wannan labari duk da girman irin wannan labari.
 
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar