BindiddigiHarkar LafiyaShin Gaskiya Ne Sama Da kashi 70% na Matasan...

Shin Gaskiya Ne Sama Da kashi 70% na Matasan Najeriya Na Shan kwaya?

-

Shekara da shekaru dai hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA na kokawa kan matsalar shaye-shaye musamman tsakanin matasa.
Shugaban hukumar Janar Buba Marwa mai ritaya ya taba bayyana cewa shaye-shaye shine yake taimakawa wajen ta’azzara matsalar tsaro a sassan Najeriya.

Ikirari

A shafin X (Twitter) wani mai suna Imran Muhammad @imranmuhdz ya wallafa rubuta da bidiyo dake nuna mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawan Najeriya Sanata Lola Ashiru yayin magana a Zauren majalisar yayi ikirarin cewa sama da kashi saba’in na matasan Najeriya na ta’ammali da kwaya.
“Ba tare dayin rowar kalamai ba sama da kashi saba’in na matasan mu na ta’ammali da kwaya, kuma a cikin yar karamar zantawa a mazaba ta wannan batu yafi karfin NDLEA, NDLEA sun zama magen lami, basu da tasiri, sabida haka barin yaki da Shan miyagun a hannun NDLEA bazai kaimu gaci ba.”

Bincike

A shekarar 2018 hukumar kididdiga ta Najeriya tare da hadin gwiwar ofishin yaki da kwayoyi da laifuka na majalisar dinkin duniya da kuma tarayyar turai sun fitar da wani rahoto dangane da ta’ammali da kwaya a Najeriya inda rahoton ya nuna cewa yan Najeriya miliyan 14.3m suke ta’ammali da kwaya a kasar wato kashi 14.4%.
Haka zalika a shakarar 2021 hukumar NDLEA tace kashi arba’in na matasa tsakanin shekaru 18-35 na ta’ammali da miyagun kwayoyi.
Wani rahoto na majalisar dinkin duniya ya kuma kara da cewa daga nan zuwa shakarar 2030 ana iya samun karin masu ta’ammali da kwayoyi zuwa miliyan 20.

Sakamako

Bayan Binciken alkaluma na yawan masu Shan miyagun kwayoyi a Najeriya dama yawan jama’ar kasar da ake kiyasta sama da miliyan dari biyu ya nuna cewa wannan ikirarin ba gaskiya bane wato false a turance.

Labarai masu alaka:

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar