BindiddigiShin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali...

Shin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali Da Nijar Daga Watan Janairu?

-

Tun bayan juyin mulkin soji a kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar kasashen uku suka sami takun saka da kungiyar ECOWAS inda suka bayyana aniyar ficewa tare da hada wata kungiyar mai suna AES. Wannan abu yazo da labaran karya da ake yadawa a kafafen sada zamunta kan kasashen dama kungiyar ta ECOWAS.

Batu:

Wani shafin kafar sada zumunta ta Tiktok mai suna @bashthausa ya wallafa wani rubutu dake ikirarin cewa; “ECOWAS ta amince da Nijar, Mali da Burkina Faso daga cikinta.”
Rubuta ya kara da cewa ficewar ta kasashen zai fara daga watan Janairun shekarar 2025.

Bincike:

Binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ya sami sanarwar tare da saurarar bayanin bayan taron na shugabannin kasashen ECOWAS da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya inda shugaban ECOWAS Oumar Tourey ya sanar da kara wa’adin amincewa da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar zuwa wata shida daga 29 ga watan Janairun 2025, domin baiwa kasashen damar ganin sun janye matakin ficewa daga kungiyar ta ECOWAS.
Sanarwar ta bayyana cewa ranar 29 ga watan Janairun itace ranar ficewa a hukumance amma an dage ranar karshe ta zama ko ficewar kasashen zuwa 29 ga watan Yuli 2025, ECOWAS dai zatayi amfani da wannan lokaci domin ganin an sulhunta tsakanin kasashen da ECOWAS.
Kasashen na Burkina Faso, Mali da Nijar dai sunce babu jada baya kan ficewa daga ECOWAS amma yan kasashe mambobin ECOWAS zasu iya shiga kasashen ba tare da visa ba kamar yadda yake a yanzu.

Sakamakon Bincike:

Bisa sauraron jawabin shugaban kungiyar ECOWAS da umar kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin akwai kamshin gaskiya.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar