BindiddigiShin Bakanuwa Ce Ta Farko Data Zama Kwamishinan ‘Yan...

Shin Bakanuwa Ce Ta Farko Data Zama Kwamishinan ‘Yan Sanda A Arewa?

-

Nuna wane ko wance sune na farko da suka zama ko suka kware kan wasu ayyuka ko fannoni na zuwa da ikiraran karya a yawancin lokuta.

Batu:

Wani shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive da shafin Facebook irin wannan suna sak Trust Radio Live ya wallafa wani hoto tare da rubuta a ranar 30/12/2024 dake cewa; “Bakanuwa ta zama ‘yar Arewa ta farko data zama kwamishinan ‘yan sanda”

Baya ga hoton dake dauke da wannan rubutu da kuma hoton ita kanta wacce ake magana akai anyi rubutu mai tsayi inda a sakin layi na farko aka rubuta cewa “ ’Yar Jihar Kano, Hauwa Ibrahim Jibrin, ta kafa tarihin samum ƙarin girma zuwa muƙamin Kwamishinan ’Yan Sanda, wanda ba a taba samun ’yar Arewa da ta kai wannan matsayi ba a tarihin Najeriya.”
Hoton wallafar shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive.
Hoton wallafar shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive.
Hoton wallafar shafin Facebook mai suna Trust Radio Live.
Hoton wallafar shafin Facebook mai suna Trust Radio Live.
Wani shafi mai suna Uzairu Lawal Rigasa shima ya wallafa irin wannan ikirari a ranar 30/12/2024 inda yace “ Bakanuwa ta zama ’Yar Arewa ta farko da ta zama Kwamishinan ’Yan sanda”

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta gano cewa kafin Hauwa Ibrahim Jibrin ta zama kwamishinan ‘yan sanda a shekarar 2024 an sami mace ‘yar arewa daga jihar Benue mai suna Farida Waziri wacce ta zama kwamishina ta zama mataimakiyar sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya AIG wanda kuma ta zama Shugabar hukumar EFCC.
Hoton Farida Waziri da mukamin AIG.
Hoton Farida Waziri da mukamin AIG.
Haka zalika binciken Alkalanci ya gano wata ‘yar arewa da aka haifa a jihar Adamawa kuma mata ga wani Basarake a jihar Taraba mai suna Aisha Abubakar Abdulwahab wacce ta zama kwamishinan ‘yan sanda a shakarar 2016 kuma ta sami karin girma zuwa mukamin mataimakiyar sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya AIG.
Hoton AIG Aisha Abubakar.
Hoton AIG Aisha Abubakar.

Sakamakon bincike:

Bisa samo mata biyu ‘yan Arewacin Najeriya daya daga Arewa maso gabas daya daga Arewa maso tsakiya da suka taba zama kwamishinan ‘yan sanda dama haurawa zuwa mukamin maitaimakin sufeta Janar AIG yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirarin karya ne.
Karin bayani: TrustRadioLive ya goge wallafar na shafin Tiktok tare da gyara wallafar shafin Facebook.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar