BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Matar Zakzaky Ce Mace Ta Farko...

Ina Gaskiyar Cewa Matar Zakzaky Ce Mace Ta Farko Data Fara Sanya Hijabi A Kasar Hausa

-

Sanya hijabi dai dabi’a ce ta Musulman duniya wanda ya hada harda Najeriya. Shekaru da dama dai Musulman Najeriya na sanya hijabi domin cika umarnin Allah da manzan sa.

Batu:

Wani shafin Facebook mai suna Safiyya Aliya ta wallafa wani hoto mai dauke da rubutun ikirarin cewa matar shugaban kungiyar Shi’a wato Ibrahim El-Zakzaky itace ta fara sanya hijabi a kasar Hausa. “Bincike  ya nuna cewa uwar gidan Sheikh El-Zakzaky ita ce ta fara sanya hijabi a kasar Hausa

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta fara da bincikar batun sanya hijabi a kasar Hausa, inda ta gano cewa Hausawa musulmi na amfani da mayafi, gyale a matsayin hijabi kamar yadda addinin musulunci ya umarci mata su lullube jikinsu.
Duk da cewa a Hausance akwai banbanci tsakanin Hijabi da mayafi ko gyale to amma dai akwai rubuce-rubuce na malaman addini a kasar Hausa da suka bayyana wasu daga cikin mayafi ko gyalen da matan Hausawa ke sawa a matsayin hijabi musamman Idan ya  cika sharrudan da addini ya shar’anta na rufe jiki.
Akwai wani bincike da aka wallafa a wani shafi mai suna African studies Center kan hijabi a arewacin Najeriya ko ace kasar Hausa. Binciken ya banbance tsakanin mayafi, gyale, layafa da hijabi inda binciken yace ana sanya hijabi a arewacin Najeriya amma an fara sanya hijabi ne sosai a farko-farkon shekarun 1970s. Binciken ya anbato kokarin marigayi Shaikh Abubakar Mahmud Gumi wajen batun sanya hijabi ya zama ruwan dare yanzu a arewacin Najeriya .
Sannan kafar bincike da bindiddigi ta Alkalanci ta gano cewa dadewar hijabi a kasar Hausa kamar dadewar musulunci ne a kasar Hausa.
Haka zalika kafar Alkalanci ta tuntubi Ibrahim Musa wanda shine babban editan jaridar Almizan wacce take mallakin mabiya Shi’a  kan gaskiyar wannan ikirari da aka alakanta da matar jagoran kungiyar Shi’a  inda yace “Salam. Ban san wanne irin bincike suka yi ba. Kuma wane irin ma’aunai suka yi amfani da shi ba wajen yin wannan ikirarin. Na san dai ‘yan’uwa ne ke fadin haka.
Amma ni a ganina zai yi wuya hakan ya zama gaskiya, saboda hijabi wani abu ne da yake cikin Musulunci. Musuluncin nan kuma akwai shi a kasar nan tun kan a haife mu.”

Sakamakon Bincike:

Bisa iya dogon bincike da kafar Alkalanci tayi na ma’anar hijabi da kuma sanya shi a kasar Hausa da kuma bincike da ma’abota ilimi sukayi babu inda aka ambato takamaimai lokacin da aka fara sanya hijabi a kasar Hausa balle wacce ta fara sanyawa.
Haka zalika batun hijabi kasancewar umarni ne na musulunci wanda musulunci ya dade matuka a kasar Hausa, kuma matan musulmi a kasar Hausa na rufe jikinsu kodai lokacin yin sallah ko zuwa unguwa tun shekaru aru-aru. Wanna yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar