BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Farfesa Maqari Ya Zama Wanda Yafi...

Ina Gaskiyar Cewa Farfesa Maqari Ya Zama Wanda Yafi Kowa Ilimin Hadisi A Afrika?

-

Suma malaman addini basu tsira ba wajen yada labaran karya akan su.

Batu:

Wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani labari cewa Farfesa Ibrahim Maqari na Najeriya ya zama dan Najeriya na farko da yafi kowa ilimin hadisi a Afrika.
Ɗan Najeriya ya zama mutum na farko da yafi kowa ilimin Hadisi a Afrika.
An zaɓi Farfesa Sheikh Prof. Ibrahim Maqari  daga Najeriya a matsayin wanda yafi kowa ilimin sanin Hadisan MANZON ALLAH SAW a kaf nahiyar Afrika. Barbara Jami’ar Musulunci ta farko wato  Al’azahar dake ƙasar Masar ta ayyana babban limamin Najeriya Professor Ibrahim Maqari a matsayin wanda yafi kowa ilimin sanin Hadisan MANZON ALLAH SAW da Fiqhu.”
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta binciki wannan ikirari inda ta gano cewa an fara yada labarin a ranar 3 ga watan Disembar 2023, yayin da shi kuma hoton an fara amfani dashi a watan Fabrairun shekarar 2022.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Sannan kafar Alkalanci ta tuntubi kanin Farfesa Ibrahim Maqari mai sun Fuad Maqari kan wannan labari dake yaduwa a kafafen sada zumunta inda ya fara tuntubar Farfesa Maqari wanda ya bashi damar yin magana a madadin sa kan wannan batu.
Fuad ya bayyanawa Alkalanci cewa; “Malam bai zo kusa da wannan batu ba, domin idan ana magana ta hadisi a Najeriya ma akwai Shaikh Shariff Saleh, kuma malamin Farfesa Maqari ne.
A yanzu Malam Sahihul Bukhari, da Muwadda Malik kawai yake karantarwa ma a fannin hadisi domin yafi mayar da hankali ga ilimin Fiqhu.”
Ya kara da cewa; “Wannan dai labarin karya ne, kuma ba labari ne da duk wani mai ilimi zai kula dashi ba, daliban malam ma dariya kawai suke. Maganar jami’ar Azhar kuwa ai ita Azhar nada malamai irin su malam sosoi, kuma Morocco da Aljeriya duk suna da irin malam dama wadanda suka fishi ilimin hadisi.”
“Tabbas kwanaki Malam yaje Morocco karbar kyauta, wannan kyauta ba tashi bace, ya karba a madadin shaikh Shariff Saleh ne. Wani abu da mutane basu sani ba ko wannan taron ma bashi da alaka da ilimin hadisi.

Sakamakon Bincike:

Kasancewar labarin dama sabun tashi akayi shekara guda bayan an fara yada shi kuma shi kansa Farfesa Maqari ta bakin kaninsa sun bayyana cewa babu wani abu makamancin haka daya faru tare da ayyana ikirarin a matsayin karya. Haka zalika babu wata kafar yada labarai sahihiya ta kowanne yare data yada irin wannan labari wanda yasa kafar bindiddigi ta Alkalanci ta yanke hukuncin cewa wannan labarin karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar