BindiddigiIna gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar...

Ina gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun bayanin ma'aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.

Iƙirari:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Comr Abba Sani Pantami ya wallafa wani iƙirari a ranar 20/03/2025 dake cewa; “Shugaban kasar Burkina Faso Ibrahim Traore ya ki yarda da bukatar Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa yace a madadin haka a yi amfani da kudaden wajen gina masa kamfanoni da koyawa matasan kasarsa sana’o’i da ayyukan dogaro da kansu.”
Wannan post dai ya sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dubu ɗaya.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Wani shafin Facebook mai suna Damagaram post shima ya wallafa wannan labarin.
Wannan labari ya sami tofa albarkacin baki sama da dari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Har ila yau wani shafi mai suna A Yau shima ya wallafa wannan labari.
Wannan wallafa ta sami tofa albarkacin baki sama da dubu ɗaya da ɗari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar tantance labarai bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntuɓi ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta Burkina Faso inda jami’in ma’aikatar yace mu duba shafin Facebook ɗin ma’aikatarinda Alkalanci ta samo bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ta Burkina faso da ta wallafa a ranar 20 ga watan Maris 2025 inda ta ƙaryata wannan labari dake yaɗuwa na cewa ƙasar Saudiyya ta wa Burkina Faso alƙawarin gina masallatai 200 wanda ita ƙasar tayi watsi da wannan buƙata.
Bayanin ya ƙara da cewa wannan rubutu an fara yaɗa shi tun a shekarar 2023, wanda ya ƙara dawowa a wannan shekarar ta 2025.
Ma’aikatar tace tun 2023 ta ƙaryata labarin, wanda bisa lura da yadda ya cigaba da yaɗuwa yasa dole aka ƙara fitar da sabuwar sanarwa.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).

Sakamakon bincike:

Bisa samun bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar