BindiddigiIna gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar...

Ina gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun bayanin ma'aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.

Iƙirari:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Comr Abba Sani Pantami ya wallafa wani iƙirari a ranar 20/03/2025 dake cewa; “Shugaban kasar Burkina Faso Ibrahim Traore ya ki yarda da bukatar Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa yace a madadin haka a yi amfani da kudaden wajen gina masa kamfanoni da koyawa matasan kasarsa sana’o’i da ayyukan dogaro da kansu.”
Wannan post dai ya sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dubu ɗaya.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Wani shafin Facebook mai suna Damagaram post shima ya wallafa wannan labarin.
Wannan labari ya sami tofa albarkacin baki sama da dari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Har ila yau wani shafi mai suna A Yau shima ya wallafa wannan labari.
Wannan wallafa ta sami tofa albarkacin baki sama da dubu ɗaya da ɗari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar tantance labarai bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntuɓi ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta Burkina Faso inda jami’in ma’aikatar yace mu duba shafin Facebook ɗin ma’aikatarinda Alkalanci ta samo bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ta Burkina faso da ta wallafa a ranar 20 ga watan Maris 2025 inda ta ƙaryata wannan labari dake yaɗuwa na cewa ƙasar Saudiyya ta wa Burkina Faso alƙawarin gina masallatai 200 wanda ita ƙasar tayi watsi da wannan buƙata.
Bayanin ya ƙara da cewa wannan rubutu an fara yaɗa shi tun a shekarar 2023, wanda ya ƙara dawowa a wannan shekarar ta 2025.
Ma’aikatar tace tun 2023 ta ƙaryata labarin, wanda bisa lura da yadda ya cigaba da yaɗuwa yasa dole aka ƙara fitar da sabuwar sanarwa.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).

Sakamakon bincike:

Bisa samun bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar