BindiddigiIna gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar...

Ina gaskiyar cewa Burkina faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun bayanin ma'aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.

Iƙirari:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Comr Abba Sani Pantami ya wallafa wani iƙirari a ranar 20/03/2025 dake cewa; “Shugaban kasar Burkina Faso Ibrahim Traore ya ki yarda da bukatar Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa yace a madadin haka a yi amfani da kudaden wajen gina masa kamfanoni da koyawa matasan kasarsa sana’o’i da ayyukan dogaro da kansu.”
Wannan post dai ya sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dubu ɗaya.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Wani shafin Facebook mai suna Damagaram post shima ya wallafa wannan labarin.
Wannan labari ya sami tofa albarkacin baki sama da dari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Har ila yau wani shafi mai suna A Yau shima ya wallafa wannan labari.
Wannan wallafa ta sami tofa albarkacin baki sama da dubu ɗaya da ɗari shida.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar tantance labarai bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntuɓi ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta Burkina Faso inda jami’in ma’aikatar yace mu duba shafin Facebook ɗin ma’aikatarinda Alkalanci ta samo bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ta Burkina faso da ta wallafa a ranar 20 ga watan Maris 2025 inda ta ƙaryata wannan labari dake yaɗuwa na cewa ƙasar Saudiyya ta wa Burkina Faso alƙawarin gina masallatai 200 wanda ita ƙasar tayi watsi da wannan buƙata.
Bayanin ya ƙara da cewa wannan rubutu an fara yaɗa shi tun a shekarar 2023, wanda ya ƙara dawowa a wannan shekarar ta 2025.
Ma’aikatar tace tun 2023 ta ƙaryata labarin, wanda bisa lura da yadda ya cigaba da yaɗuwa yasa dole aka ƙara fitar da sabuwar sanarwa.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin karyata labarin a harshen Faransanci.
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).
Hoton bayanin Burkina Faso na karyata labarin gina masallatai 200 (Fassarar Turanci).

Sakamakon bincike:

Bisa samun bayanin ma’aikatar harkokin ƙasashen wajen ƙasar Burkina Faso na ƙaryata wannan labari tare da bayanin cewa labarin ya daɗe yana yawo tsakanin mutane, kuma Saudiyya bata gabatar da wannan bukata ba. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa, iƙirarin cewa ƙasar Burkina Faso tayi watsi da buƙatar Saudiyya na gina masallatai 200 ƙarya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar