BindiddigiIna Gaskiyar cewa Asiya Sulaiman Ibrahim Itace Mace Ta...

Ina Gaskiyar cewa Asiya Sulaiman Ibrahim Itace Mace Ta Farko Data Kammala Karatun Digiri A Yankin Falgore?

-

Garin Falgoren Daji dake karamar hukumar Doguwa gari ne dake bakin dajin daya hada jihar Kano da Bauchi kuma ya hade da dajin Yankari. Gari ne dake da kasuwa inda ake siye da siyarwar kayan noma da dabbobi.

Batu:

Akwai wani ikirari da wani shafin Facebook mai suna RFI Hausa ya wallafa wani bidiyo mai tsawon mintuna biyu tare da rubuta cewa wata mata dake bidiyon itace mace ta farko data kammala karatun digiri a yankin Falgore karamar hukumar Doguwa dake jihar Kano.
Mace ta farko da ta kammala karatun digiri a yankin Falgore dake karamar hukumar Doguwa a jihar Kanon Najeriya.”
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta fara bincika kafin ita wannan mata a bidiyo da akai ikirari akwai mace ‘yar wannan gari ta Falgore data kammala karatun digiri? Alkalanci mun gano cewa akwai mata da suka kai akalla hudu da suke yan asalin wannan gari na Falgore ne kuma sun kammala karatun digiri shekaru kafin ita wacce aka wallafa a bidiyon wacce ko hidimar kasa wato NYSC ma batayi ba.
Mun tuntubi wani dan asalin wannan gari na Falgore kuma ma’aikaci a jami’ar ABU mai suna  Nuraddeen Adam Iliyasu wanda yace; “Akwai mata ‘yan asalin garin Falgore da suka kammala jami’a. Ina farin ciki cewa ita wannan mata mai suna Asiya ‘yar garin namu na Falgore  ta kammala digiri amma batun cewa ita ta farko bai taso ba.”
Ga sunayen wasu daga cikin matan da ‘yan asalin wannan gari na Falgore ne, kuma sun kammala  karatun digiri.
  1.  Hadiza Ibrahim BSc. Adult Education 2018
  2.  Halima Ibrahim Yusuf BSc. Nursing (BUK)2021
  3. Bushira Garba Abdu B.Ed (ABU)2023
  4. Hajara Ibrahim BSc. English (BUK)2020
Ya kara da cewa, “dukkan su Idan anzo karbar tallafin karatu wato scholarship takardun shaidar gari na asali dama karamar hukuma duk na Falgore da karamar hukumar Doguwa ne.”
A ikirarin ance yankin Falgore wanda hakan ke nufin garuruwan dake kusa da Falgore inda Nuraddeen ya kara da cewa; “Yankin Falgore suna nufin Idan ka hauro daga daji kenan, to ya zasuyi da mata da yawa da suka kammala digiri ‘yan asalin garin Burji?”

Sakamakon Bincike:

Bisa samun bayani daga ‘yan wannan gari tare da tabbatar da cewa wadancan sunaye ‘yan asalin wancan gari na Falgore ne, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin RFI Hausa na cewa Asiya itace mace ta farko data kammala digiri daga yankin Falgore karya ne.

Labarai masu alaka: 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar