BindiddigiGaskiyane Sanata Akpabio Yayi Sallah A Masallacin Kasa?

Gaskiyane Sanata Akpabio Yayi Sallah A Masallacin Kasa?

-

Masallacin kasa wato National Mosque dake Abuja dai gurin ibadane da mafi kasarin lokuta shugabanni ke zuwa yin ibada ko daura auren ‘ya’yansu.

Batu:

Ranar Juma’ar data gabata ne dai aka hango shugaban Najeriya, Bola Tinubu, shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, wanda ba musulmi ba, kakakin majalisar wakilai Tajuddeen Abbas, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da sauran manyan mutane a zaune a sahun gaba a masallacin kasa.

Bayan bullar wannan hoto ne dai aka farun samun masu tofa albarkacin bakinsu kan wannan batu inda wani mai amfani da Facebook mai suna Shehu Tijjani Shareef

 ya rubuta cewa (archived here) “Akpabio a Masallaci Muslim-Muslim ta fara muluntar da jami’an gwamnati.”

Wannan wallafa ta sami mutane da dama da suka tofa albarkacin bakinsu tare da aminta da abinda ya rubuta misali; Imrana Auwal Dan So yace “Masha Allah mulkin Tinubu anci riba sosai.”

An dai sami ire-iren wannan wallafa dake nuna cewa shugaban majalisar dattawa Akpabio yayi Sallah a sahun gaba. Misali wani mai suna Muhammad Tukur Usman yace (archived here)“ Wato magana ake ta Mulki Kawai a Abuja😀😀 Senate President ne a Masallaci( Godwin Akpabio) Kuma a sahun gaba.“

Shima Sa’ad Matawalle cewa yayi (archived here) “Babban cigaban da muslim muslim ticket ta kawo shine shiga da AKPABIO cikin masallaci.🙄😭“

Bincike:

Binciken Alkalanci ya gano cewa shugaban majalisar bai shiga masallacin don zama musulmi Ko yin Sallah ba fyace yaje domin shaida daurin auren yar Sanata Danjuma mai suna Fauziyya.

Sakamakon Bincike:

Bisa binciken da Alkalanci yayi ya tabbatar da cewa zuwan Sanata Akpabio Masallacin Kasa da zama a gaba bashi da alaka da ibadar sallah Ko zama musulmi face shaidar daurin auren ‘yar daya daga cikin Santocin daya ke jagoranta. Wannan yasa ikirari ya zama karya wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar