BindiddigiGaskiyane Sanata Akpabio Yayi Sallah A Masallacin Kasa?

Gaskiyane Sanata Akpabio Yayi Sallah A Masallacin Kasa?

-

Masallacin kasa wato National Mosque dake Abuja dai gurin ibadane da mafi kasarin lokuta shugabanni ke zuwa yin ibada ko daura auren ‘ya’yansu.

Batu:

Ranar Juma’ar data gabata ne dai aka hango shugaban Najeriya, Bola Tinubu, shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, wanda ba musulmi ba, kakakin majalisar wakilai Tajuddeen Abbas, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da sauran manyan mutane a zaune a sahun gaba a masallacin kasa.

Bayan bullar wannan hoto ne dai aka farun samun masu tofa albarkacin bakinsu kan wannan batu inda wani mai amfani da Facebook mai suna Shehu Tijjani Shareef

 ya rubuta cewa (archived here) “Akpabio a Masallaci Muslim-Muslim ta fara muluntar da jami’an gwamnati.”

Wannan wallafa ta sami mutane da dama da suka tofa albarkacin bakinsu tare da aminta da abinda ya rubuta misali; Imrana Auwal Dan So yace “Masha Allah mulkin Tinubu anci riba sosai.”

An dai sami ire-iren wannan wallafa dake nuna cewa shugaban majalisar dattawa Akpabio yayi Sallah a sahun gaba. Misali wani mai suna Muhammad Tukur Usman yace (archived here)“ Wato magana ake ta Mulki Kawai a Abuja😀😀 Senate President ne a Masallaci( Godwin Akpabio) Kuma a sahun gaba.“

Shima Sa’ad Matawalle cewa yayi (archived here) “Babban cigaban da muslim muslim ticket ta kawo shine shiga da AKPABIO cikin masallaci.🙄😭“

Bincike:

Binciken Alkalanci ya gano cewa shugaban majalisar bai shiga masallacin don zama musulmi Ko yin Sallah ba fyace yaje domin shaida daurin auren yar Sanata Danjuma mai suna Fauziyya.

Sakamakon Bincike:

Bisa binciken da Alkalanci yayi ya tabbatar da cewa zuwan Sanata Akpabio Masallacin Kasa da zama a gaba bashi da alaka da ibadar sallah Ko zama musulmi face shaidar daurin auren ‘yar daya daga cikin Santocin daya ke jagoranta. Wannan yasa ikirari ya zama karya wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar