BindiddigiBidiyon Shekarar 2013 Na Sojojin Najeriya Dana Faransa A...

Bidiyon Shekarar 2013 Na Sojojin Najeriya Dana Faransa A Mali Na Yaduwa A Matsayin Sabo

-

Tun bayan sabon zarge-zarge da gwamnatin kasar Nijar tawa gwamnatin Najeriya kan samar da sansanin sojin Faransa a wani yanki na arewacin Najeriya aka kara samun karuwar ikiraran karya a kafafafen sada zamunta.

Batu:

Wani shafin Facebook mai suna IG Wala ya wallafa tsohon wani  (archived here) bidiyo ranar 27/12/2024 dake nuna sojin Najeriya dana Faransa suna kwasar kaya daga jirgin sama inda ana iya ganin jirgin sojin Najeriya a bidiyon wanda ya rubuta cewa “Wadanne ‘yan gudun hijira ne wadannan masu kama da sojojin Faransa a Nigeria?😎 #Bamayi2027
Mutane sama da dubu goma sha daya ne suka kalla a lokacin hada wannan bincike yayin da sama da mutane dari da tamanin sukai shares.
Shima wani shafin na Facebook mai suna Grema Karagama ya wallafa bidiyon (archived here) ranar 29/12/2024 inda yake ikirarin cewa “ANOTHER ONE:💥💥💥 Ashe da gaske dai Sojojin Faransa sun shigo NIGERIA 😱😭

Haka shima wani shafi mai suna Usman Aljabbari Algwambawi ya wallafa wannan bidiyo ranar 27/12/2024 inda ya rubuta cewa “ Innalillahi wanna ilayihi rajiuna jama ar arewa mu qara Adu a sojojin faransa sun sigo arewa ccin Najeriya 😭😭

Shima wani wani shafi mai suna Hashim Danbala ya wallafa bidiyon ranar  (archived here) 28/12/2024 inda ya rubuta cewa “ Ashe da gaske dai Sojojin Faransa sun shigo NIGERIA 😢🥸

Bincike:

Da kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta sanya bidiyon a wata manhaja ta gano cewa tsohon bidiyo ne da kafar dillancin labarai ta AP ta dauka kuma ya fara shiga yanar gizo ne tun a shekarar 2013 yayin da sojoji harda na Najeriya suka  sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na Senou dake Bamako domin zuwa aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Mali.
Sojan Najeriya da aka gani yana magana a bidiyon dai Birgediya Janar Sa’ad Hanafi Abubakar mai ritaya ne wanda ya bar aikin soji tun shekarar 2016.
Haka zalika cikin jawabin sojin kasar Faransa a cikin bidiyo inda masana harshen Faransanci suka fassarawa Alkalanci anji yana cewa “akwai sojin Najeriya 156, sojin kasar Togo 100, 25 daga kasar Benin kuma ana sa ran zuwan wasu 25 daga kasar ta Benin daran yau.

Sakamakon Bincike:

Bisa la’akari da cewa bidiyon ya haura shekara goma da dauka, haka zalika duk faya-fayen bidiyon  da aka dinga yadawa harda wanda Alkalanci tayi bincike kwanakin baya inda ta gano sojin Birtaniya ne. Yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin dake saman tsohon bidiyon karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar