Fayyace abubuwaAbinda ya kamata ku sani dangane da zaɓen shugaban...

Abinda ya kamata ku sani dangane da zaɓen shugaban kasar Kamaru

-

A ranar asabar mai zuwa ne dai al’ummar ƙasar Kamaru zasu je runfunan zaɓe domin zaɓen shugaban ƙasa.

Shugaban ƙasar mai ci Paul Biya na neman a kara zaɓen sa. Duk da cewa ‘yar sa a kwanakin baya ta yi kira ga ‘yan kasar da kada su zabi mahaifin nata.
Ga wasu alƙaluma dangane da zaɓen wanda muka samo daga hukumar zaɓen ƙasar ta Kamaru.
Shugabanni nawa aka taba yi tun bayan samun yancin kai?
 
Tun samun ƴancin kai a shekarar 1960 shugabanni biyu kacal ne sukayi mulkin shugabancin ƙasar.
Ahmadou Ahidjo wanda ya mulki ƙasar daga 1960 zuwa 1984 wato yayi shekaru 24 yana mulkar Kamaru.
Paul Biya ya fara mulki daga shekarar 1984 zuwa yanzu.
Yawan masu kada kuri’a 
Ƴan ƙasar miliyan 8 da dubu ɗari biyu (8.2m)  ne suka yi rijistar zaɓe. Kashi hamsin da hudu (54%) maza ne. Mata na da kashi arba’in da shida ((46%)
Yan takara nawa ne?
Akwai ƴan takara goma dake neman kujerar shugaban ƙasar ta Kamaru ciki har da shugaba mai ci Paul Biya mai shekaru 92.
Sai kuma wani matashi Hiram Samuel Iyodi mai shekaru 38.
Akwai kuma Issa Tchiroma Bakary da haɗakar wasu jam’iyyun adawa suka fitar wanda ya fito daga Garoua dake arewacin Kamaru. Ya kasance tsohon mai magana da yawan gwamnatin ƙasar.
Bello Bouba Maigari tsohon ministan yawan buɗe ido na ƙasar ta Kamaru.
Akwai kuma mace tilo dake naman takarar zama shugabar Kamaru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar