BindiddigiShin Bakanuwa Ce Ta Farko Data Zama Kwamishinan ‘Yan...

Shin Bakanuwa Ce Ta Farko Data Zama Kwamishinan ‘Yan Sanda A Arewa?

-

Nuna wane ko wance sune na farko da suka zama ko suka kware kan wasu ayyuka ko fannoni na zuwa da ikiraran karya a yawancin lokuta.

Batu:

Wani shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive da shafin Facebook irin wannan suna sak Trust Radio Live ya wallafa wani hoto tare da rubuta a ranar 30/12/2024 dake cewa; “Bakanuwa ta zama ‘yar Arewa ta farko data zama kwamishinan ‘yan sanda”

Baya ga hoton dake dauke da wannan rubutu da kuma hoton ita kanta wacce ake magana akai anyi rubutu mai tsayi inda a sakin layi na farko aka rubuta cewa “ ’Yar Jihar Kano, Hauwa Ibrahim Jibrin, ta kafa tarihin samum ƙarin girma zuwa muƙamin Kwamishinan ’Yan Sanda, wanda ba a taba samun ’yar Arewa da ta kai wannan matsayi ba a tarihin Najeriya.”
Hoton wallafar shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive.
Hoton wallafar shafin Tiktok mai suna TrustRadioLive.
Hoton wallafar shafin Facebook mai suna Trust Radio Live.
Hoton wallafar shafin Facebook mai suna Trust Radio Live.
Wani shafi mai suna Uzairu Lawal Rigasa shima ya wallafa irin wannan ikirari a ranar 30/12/2024 inda yace “ Bakanuwa ta zama ’Yar Arewa ta farko da ta zama Kwamishinan ’Yan sanda”

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta gano cewa kafin Hauwa Ibrahim Jibrin ta zama kwamishinan ‘yan sanda a shekarar 2024 an sami mace ‘yar arewa daga jihar Benue mai suna Farida Waziri wacce ta zama kwamishina ta zama mataimakiyar sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya AIG wanda kuma ta zama Shugabar hukumar EFCC.
Hoton Farida Waziri da mukamin AIG.
Hoton Farida Waziri da mukamin AIG.
Haka zalika binciken Alkalanci ya gano wata ‘yar arewa da aka haifa a jihar Adamawa kuma mata ga wani Basarake a jihar Taraba mai suna Aisha Abubakar Abdulwahab wacce ta zama kwamishinan ‘yan sanda a shakarar 2016 kuma ta sami karin girma zuwa mukamin mataimakiyar sufeta Janar na ‘yan sandan Najeriya AIG.
Hoton AIG Aisha Abubakar.
Hoton AIG Aisha Abubakar.

Sakamakon bincike:

Bisa samo mata biyu ‘yan Arewacin Najeriya daya daga Arewa maso gabas daya daga Arewa maso tsakiya da suka taba zama kwamishinan ‘yan sanda dama haurawa zuwa mukamin maitaimakin sufeta Janar AIG yasa kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirarin karya ne.
Karin bayani: TrustRadioLive ya goge wallafar na shafin Tiktok tare da gyara wallafar shafin Facebook.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar