BindiddigiShin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali...

Shin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali Da Nijar Daga Watan Janairu?

-

Tun bayan juyin mulkin soji a kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar kasashen uku suka sami takun saka da kungiyar ECOWAS inda suka bayyana aniyar ficewa tare da hada wata kungiyar mai suna AES. Wannan abu yazo da labaran karya da ake yadawa a kafafen sada zamunta kan kasashen dama kungiyar ta ECOWAS.

Batu:

Wani shafin kafar sada zumunta ta Tiktok mai suna @bashthausa ya wallafa wani rubutu dake ikirarin cewa; “ECOWAS ta amince da Nijar, Mali da Burkina Faso daga cikinta.”
Rubuta ya kara da cewa ficewar ta kasashen zai fara daga watan Janairun shekarar 2025.

Bincike:

Binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ya sami sanarwar tare da saurarar bayanin bayan taron na shugabannin kasashen ECOWAS da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya inda shugaban ECOWAS Oumar Tourey ya sanar da kara wa’adin amincewa da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar zuwa wata shida daga 29 ga watan Janairun 2025, domin baiwa kasashen damar ganin sun janye matakin ficewa daga kungiyar ta ECOWAS.
Sanarwar ta bayyana cewa ranar 29 ga watan Janairun itace ranar ficewa a hukumance amma an dage ranar karshe ta zama ko ficewar kasashen zuwa 29 ga watan Yuli 2025, ECOWAS dai zatayi amfani da wannan lokaci domin ganin an sulhunta tsakanin kasashen da ECOWAS.
Kasashen na Burkina Faso, Mali da Nijar dai sunce babu jada baya kan ficewa daga ECOWAS amma yan kasashe mambobin ECOWAS zasu iya shiga kasashen ba tare da visa ba kamar yadda yake a yanzu.

Sakamakon Bincike:

Bisa sauraron jawabin shugaban kungiyar ECOWAS da umar kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin akwai kamshin gaskiya.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar