BindiddigiShin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali...

Shin ECOWAS Ta Amince Da Ficewar Burkina Faso, Mali Da Nijar Daga Watan Janairu?

-

Tun bayan juyin mulkin soji a kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar kasashen uku suka sami takun saka da kungiyar ECOWAS inda suka bayyana aniyar ficewa tare da hada wata kungiyar mai suna AES. Wannan abu yazo da labaran karya da ake yadawa a kafafen sada zamunta kan kasashen dama kungiyar ta ECOWAS.

Batu:

Wani shafin kafar sada zumunta ta Tiktok mai suna @bashthausa ya wallafa wani rubutu dake ikirarin cewa; “ECOWAS ta amince da Nijar, Mali da Burkina Faso daga cikinta.”
Rubuta ya kara da cewa ficewar ta kasashen zai fara daga watan Janairun shekarar 2025.

Bincike:

Binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ya sami sanarwar tare da saurarar bayanin bayan taron na shugabannin kasashen ECOWAS da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya inda shugaban ECOWAS Oumar Tourey ya sanar da kara wa’adin amincewa da ficewar kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar zuwa wata shida daga 29 ga watan Janairun 2025, domin baiwa kasashen damar ganin sun janye matakin ficewa daga kungiyar ta ECOWAS.
Sanarwar ta bayyana cewa ranar 29 ga watan Janairun itace ranar ficewa a hukumance amma an dage ranar karshe ta zama ko ficewar kasashen zuwa 29 ga watan Yuli 2025, ECOWAS dai zatayi amfani da wannan lokaci domin ganin an sulhunta tsakanin kasashen da ECOWAS.
Kasashen na Burkina Faso, Mali da Nijar dai sunce babu jada baya kan ficewa daga ECOWAS amma yan kasashe mambobin ECOWAS zasu iya shiga kasashen ba tare da visa ba kamar yadda yake a yanzu.

Sakamakon Bincike:

Bisa sauraron jawabin shugaban kungiyar ECOWAS da umar kafar Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin akwai kamshin gaskiya.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar