BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Farfesa Maqari Ya Zama Wanda Yafi...

Ina Gaskiyar Cewa Farfesa Maqari Ya Zama Wanda Yafi Kowa Ilimin Hadisi A Afrika?

-

Suma malaman addini basu tsira ba wajen yada labaran karya akan su.

Batu:

Wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani labari cewa Farfesa Ibrahim Maqari na Najeriya ya zama dan Najeriya na farko da yafi kowa ilimin hadisi a Afrika.
Ɗan Najeriya ya zama mutum na farko da yafi kowa ilimin Hadisi a Afrika.
An zaɓi Farfesa Sheikh Prof. Ibrahim Maqari  daga Najeriya a matsayin wanda yafi kowa ilimin sanin Hadisan MANZON ALLAH SAW a kaf nahiyar Afrika. Barbara Jami’ar Musulunci ta farko wato  Al’azahar dake ƙasar Masar ta ayyana babban limamin Najeriya Professor Ibrahim Maqari a matsayin wanda yafi kowa ilimin sanin Hadisan MANZON ALLAH SAW da Fiqhu.”
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta binciki wannan ikirari inda ta gano cewa an fara yada labarin a ranar 3 ga watan Disembar 2023, yayin da shi kuma hoton an fara amfani dashi a watan Fabrairun shekarar 2022.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Sannan kafar Alkalanci ta tuntubi kanin Farfesa Ibrahim Maqari mai sun Fuad Maqari kan wannan labari dake yaduwa a kafafen sada zumunta inda ya fara tuntubar Farfesa Maqari wanda ya bashi damar yin magana a madadin sa kan wannan batu.
Fuad ya bayyanawa Alkalanci cewa; “Malam bai zo kusa da wannan batu ba, domin idan ana magana ta hadisi a Najeriya ma akwai Shaikh Shariff Saleh, kuma malamin Farfesa Maqari ne.
A yanzu Malam Sahihul Bukhari, da Muwadda Malik kawai yake karantarwa ma a fannin hadisi domin yafi mayar da hankali ga ilimin Fiqhu.”
Ya kara da cewa; “Wannan dai labarin karya ne, kuma ba labari ne da duk wani mai ilimi zai kula dashi ba, daliban malam ma dariya kawai suke. Maganar jami’ar Azhar kuwa ai ita Azhar nada malamai irin su malam sosoi, kuma Morocco da Aljeriya duk suna da irin malam dama wadanda suka fishi ilimin hadisi.”
“Tabbas kwanaki Malam yaje Morocco karbar kyauta, wannan kyauta ba tashi bace, ya karba a madadin shaikh Shariff Saleh ne. Wani abu da mutane basu sani ba ko wannan taron ma bashi da alaka da ilimin hadisi.

Sakamakon Bincike:

Kasancewar labarin dama sabun tashi akayi shekara guda bayan an fara yada shi kuma shi kansa Farfesa Maqari ta bakin kaninsa sun bayyana cewa babu wani abu makamancin haka daya faru tare da ayyana ikirarin a matsayin karya. Haka zalika babu wata kafar yada labarai sahihiya ta kowanne yare data yada irin wannan labari wanda yasa kafar bindiddigi ta Alkalanci ta yanke hukuncin cewa wannan labarin karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar