BindiddigiShin Shugaban Senegal Ya Bukaci Putin Yasa Kasashen Burkina...

Shin Shugaban Senegal Ya Bukaci Putin Yasa Kasashen Burkina Faso, Mali, Nijar Su Koma ECOWAS?

-

Labarun karya da na kawar da hankulan mutane dai na cigaba da yaduwa a kafafen sada zumunta musamman kan halin da ake ciki a yammacin Afrika da wasu yankunan Sahel.

Ikirari:

Wani matashi ya wallafa wani bidiyo mai tsawon minti daya da sakan arba’in (adana bayanai a NAN) da ku a shafinsa na TikTok mai suna @kebi.ne inda yake ikirarin cewa shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya zanta da shugaban Rasha Vladimir Putin inda ya bukaci Putin daya sa shugabannin kasashe Burkina Faso, Mali da Nijar su koma kungiyar ECOWAS.
Shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye ya tafka abin kunya ga kasashen mu na AES. Abunda ake ta tafka mahawara a kafafen sadarwa shine aikin da yayi na kiran shugaban Rasha Vladimir Putin akan ya bawa kasashe AES shawara kan su koma tsohuwar kungiyar nan ta ECOWAS…”
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa

Bincike:

A binciken kafar bindiddigi ta Alkalanci ta samo bayanin tattaunar da shugabannin kasashen biyu na Senegal da Rasha sukayi a shafin gwamnatin kasar Rashar.

Rasha tace zantawar anyi tane kan yadda kasashen biyu zasu karfafa alaka ta kawance, tattalin arziki, kasuwanci, noma da fannin sufuri. Sanarwar ta kara da cewa shugaban Senegal ya bukaci samun sana’o’in Rasha a kasar sa domin cigaba. Inda shugaba Putin ya gayyaci shugaban Senegal zuwa Rasha inda ya amince.

Har ila yau shafin gwamnatin kasar Senegal shima ya wallafa bayanin tattaunawar inda yace anyi tane kan batun karfafa kawance da yadda za’a kawo karshen matsalar tsaro a yammacin Afrika.
Kafafen yada labarai na duniya duk sun rawaito labarin tattaunawar amma kan batun tsaro da tattalin arziki tare da gayyatar da Putin yawa shugaban na Senegal.

Sakamakon Bincike:

Binciken kafar Alkalanci dai bai sami guri daya da aka ambato cewa shugaban kasar Senegal ya bukaci Putin daya sanya baki kan kasashen AES su koma ECOWAS ba. Sannan babu wani gidan jarida ko daya da ya kawo irin wannan ikirari. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirarin karya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar