BindiddigiYaushe Khadijah AbdulHameed Taki Musabaha Da Shugaban Bankin UBA?

Yaushe Khadijah AbdulHameed Taki Musabaha Da Shugaban Bankin UBA?

-

Gidauniyar bankin UBA dai na daukar nauyin gasar rubutun insha’i wato essay competition, shekaru sama da goma, wanda yara ‘yan makaranta kan shiga.

Batu:

A tsakanin asabar 23 zuwa lahadi 24 ga watan Nuwamban shekarar 2024 ana ta yada hoton wata yarinyar mai suna Khadijah AbdulHameed wacce ake ikirarin taki yin masabaha da shugaban bankin UBA bayan tazo na biyu a gasar saboda addininta na musulunci bai bata dama ba.
Wani shafin Facebook mai suna Jaridar Arewa ya wallafa wannan labari a ranar lahadi 24/11/2024 a matsayin labarin daya faru a ranar. “ DA ƊUMI-ƊUMI: “Addini na ya hana hakan” Khadijah taƙi amincewa da musafaha da shugaban bankin UBA Sunanta Khadijah Abdulhamid, Husna daga makarantar Sakandaren Sweet Haven ta Jihar Kano, ta ki amincewa da musafaha da Oliver Alawuba, Shugaban Kamfanin UBA, a wajen gabatar da lambar yabo ta UBA Foundation Nigeria, inda ta ce Addininta ya hana hakan. Daga Usman Umar Katsina
Wannan hoto dai na cigaba da yaduwa inda ake nuna cewa abun ya faru ne a wannan shekarar ta 2024.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi Alkalanci ta bincika hoton inda ta samo cewa wannan hoto an fara yada shine a watan Nuwamban bara wato 2023 lokacin da Khadijah AbdulHameed tazo ta biyu a gasar gidauniyar UBA karo na goma sha uku. A gasar dai Khadija ta sami kyautar Naira miliyan Uku.
A wancan lokaci mutane da dama sun yada wannan hoto dauke da bayanin yadda taki yin musabahar.
Alkalanci ta bincika hoton inda ta samo cewa wannan hoto an fara yada shine a watan Nuwamban bara wato 2023
Alkalanci ta bincika hoton inda ta samo cewa wannan hoto an fara yada shine a watan Nuwamban bara wato 2023

Sakamakon Bincike:

Binciken kafar Alkalanci ta tabbatar da cewa tabbas hoton gaskiya kuma ya faru, kuma Khadijah ta wakilci makarantar ta Sweet Haven dake Kano, to amma ba a wannan shekarar ta 2024 ne ya faru ba. Don haka ikirarin ko labarin dake nuna a wannan shekara ta 2024 abun ya faru ba gaskiya bane.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar