BindiddigiShin Gaskiyane Mali Ta Fita Daga Kangin Bashin Kasashen...

Shin Gaskiyane Mali Ta Fita Daga Kangin Bashin Kasashen Waje?

-

Hausawa sukace bashi hanji ne… wato yana cikin kowa- Kasashen Afirka na cikin kasashen duniya dake karbar basussuka daga bankunan kasa da kasa dama kasashe kansu.

Batu:

Wani shafi mai suna Daily News Hausa 24 ya wallafa cewa; “ A daidai lokacin da Nigeria ke kara ciyo dinbin bashi daga kasashen waje, sai gashi  Yanzu haka ƙasar Mali babu kasar da ke binta bashi duk duniya.
Yaushe kuke ganin Nigeria za ta gama biyan bashin da ake bin ta ?”
Wasu shafuka sun wallafa irin wannan rubutu kuma ya sami shares da dama.

Bincike:

Alkalanci yayi bincike kan wannan ikirari inda muka fara da duba kome asusun bada lamuni na IMF ke cewa Kan bashin da ake bin kasar Malin.
Mun gano cewa ya zuwa shekarar 2022 bashin kasashen waje dake kan kasar Mali ya haura dala biliyan shida ($6,342,843,423)) a bara dai asusun bada lamunin na IMF ya nuna damuwa kan yadda Mali ke samun karuwar basussuka.
Sannan mun duba shafin bankin duniya inda muka samo jerin bankuna dama kasashen dake bin kasar Mali bashin wanda ya hada da bankin duniya, bankin bunkasa Afrika, bankin bunkasa yammacin Afrika, gwamnatin Faransa, Chana, Indiya, Abu Dhabi. Kuma kashi 30 na bashin daga kasashen wajen a kudin Euro ne a cewar rahoton bankin duniya.
Bamu tsaya anan ba mun bincika me ita gwamnatin Mali ke cewa Kan basussuka, sai muka samo bayanin ministan tattalin arzikin kasar Alousseni Sanou inda yace kasar na kokarin biyan bashin cikin gida daya kai dala miliyan dari uku da talatin da uku ($332 million).
Sannan bankin bunkasa nahiyar Afrika ya fitar da jerin kasashen da bashinsu bashi da yawa wanda kasar ta Mali bata ciki.

 

Sakamakon Bincike:

Bisa wadannan alkaluma da bincike da Alkalanci yayi inda ya kasa samo sahihan labari Ko ikirari dake nuna cewa kasar ta Mali ta zama kasar da ba’a binta  bashi ya nuna cewa wannan labari karya ne domin kuwa babu wata kafar yada labarai sananniya a Afrika Ko a wajen Afrika data rawaito wannan labari duk da girman irin wannan labari.
 
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar