BindiddigiHarkar LafiyaShin Gaskiya Ne Sama Da kashi 70% na Matasan...

Shin Gaskiya Ne Sama Da kashi 70% na Matasan Najeriya Na Shan kwaya?

-

Shekara da shekaru dai hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA na kokawa kan matsalar shaye-shaye musamman tsakanin matasa.
Shugaban hukumar Janar Buba Marwa mai ritaya ya taba bayyana cewa shaye-shaye shine yake taimakawa wajen ta’azzara matsalar tsaro a sassan Najeriya.

Ikirari

A shafin X (Twitter) wani mai suna Imran Muhammad @imranmuhdz ya wallafa rubuta da bidiyo dake nuna mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawan Najeriya Sanata Lola Ashiru yayin magana a Zauren majalisar yayi ikirarin cewa sama da kashi saba’in na matasan Najeriya na ta’ammali da kwaya.
“Ba tare dayin rowar kalamai ba sama da kashi saba’in na matasan mu na ta’ammali da kwaya, kuma a cikin yar karamar zantawa a mazaba ta wannan batu yafi karfin NDLEA, NDLEA sun zama magen lami, basu da tasiri, sabida haka barin yaki da Shan miyagun a hannun NDLEA bazai kaimu gaci ba.”

Bincike

A shekarar 2018 hukumar kididdiga ta Najeriya tare da hadin gwiwar ofishin yaki da kwayoyi da laifuka na majalisar dinkin duniya da kuma tarayyar turai sun fitar da wani rahoto dangane da ta’ammali da kwaya a Najeriya inda rahoton ya nuna cewa yan Najeriya miliyan 14.3m suke ta’ammali da kwaya a kasar wato kashi 14.4%.
Haka zalika a shakarar 2021 hukumar NDLEA tace kashi arba’in na matasa tsakanin shekaru 18-35 na ta’ammali da miyagun kwayoyi.
Wani rahoto na majalisar dinkin duniya ya kuma kara da cewa daga nan zuwa shakarar 2030 ana iya samun karin masu ta’ammali da kwayoyi zuwa miliyan 20.

Sakamako

Bayan Binciken alkaluma na yawan masu Shan miyagun kwayoyi a Najeriya dama yawan jama’ar kasar da ake kiyasta sama da miliyan dari biyu ya nuna cewa wannan ikirarin ba gaskiya bane wato false a turance.

Labarai masu alaka:

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar