BindiddigiShin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya...

Shin shugaban kasar Korea ta arewa yace zai iya gyara Najeriya cikin shakara daya?

-

Gabatarwa

Shekaru da dama dai yan Najeriya na ganin cewa kasar bata kan turbar dai-dai wato tana bukatar saiti ko ace gyara, musamman yadda ake fito da yadda aka sami wasu da suka rike shugabanci da almundahan tare da yin rub-da-ciki da kudaden yan kasar.

Wasu kasashe dai musamman a Asiya nada tsarin hukunci mai tsauri ga duk shugaban da aka samu da cin hanci Ko rashawa. Kasar Koriya ta arewa na cikin kasashen da mutane ke ganin cewa shugaban kasar baya wasa da batun doka da oda da kuma tabbatar da kasar ta sami cigaba da fannin mallakar makamai wanda ya hada da makamin kare dangi na nuclear.

Ikirari

Wani shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa ya wallafa wani rubutu tare da hoton shugaban kasar Korea ta arewa inda rubutun ke cewa;
“Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal. Kuma idan aka ba ni Nijeriya na yi masu mulkin mallaka, a cikin shekara daya zan mayar da su cikin rukunin manyan kasashen duniya, Cewar matashin Shugaban Kasar Koriya ta Arewa Kin Jong Un. Me za ku ce?”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Wannan rubutu ya sami yadawa wato shares sama da dari uku yayin da mutane da dama suka bayyana nasu ra’ayin.
Misali Yusuf Musa Numan yace “Ni nasan da hakan zai kasance tabbas zaka iya gyara Najeriya.”

A shafin X wato Twitter wata mai lakabin @Ameenatu_ itama ta wallafa irin wancan post inda yake cewa; “Zan iya gyara Najeriya cikin shekara daya kacal-Inji shugaban Koriya ta arewa Kim Jong Un.”

Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.
Hoton rubutun da aka wallafa dake cigaba da yaduwa.

Mutane sama da dari biyu ne suka tofa albarkacin bakinsu yayin da mutane sama da dadi bakwai suka danna like.
Bincike

An taba wallafa makamancin wannan kalamai a shekarar 2018 wanda Binciken da kafar jarida ta ICIR tayi ya nuna cewa wani shafi mai yada labaran karya da farfaganda mai suna Aljazeera West Africa ce ta fara wallafa shi. Saboda rashin shaida za’a iya cewa wancan labarin na aka sabunta ya dawo domin cimma wata manufa.

Sakamakon Bincike

Bincike da alkalanci yayi ya nuna cewa wannan bayani karya ne kawai, wato false a turance.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar