BindiddigiIna gaskiyar cewa babu sojin ƙasar waje a Nijar

Ina gaskiyar cewa babu sojin ƙasar waje a Nijar

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa kasa samun inda hukumomin Nijar da Rasha suka bayyana ficewar sojin da suka zo Nijar shekarar data gabata suka kuma maye gurbin sansanin sojin Amurka, Sannan ƴan jaridu da mutanen a garin Tilliberi sun tabbatar da ganin sojin Rasha lokacin da shugaban ƙasar Nijar Tiani yakai ziyara. Haka zalika an gano sojin ƙasashen waje a bidiyon taron yaye sojojin ƙasar ta Nijar a satin daya gabata. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin babu sojin ƙasashen waje a Nijar jirkata bayani ne wato misleading a turance.

Juyin mulkin da soji sukayi a ƙasar Nijar ya janyo takun saƙa da wasu ƙasashe.

Ƙasar ta Nijar dai ta fice daga ƙungiyar ECOWAS tare da korar sojin ƙasashen Faransa da Amurka.

Nijar dai ta ƙarfafa alaƙa da ƙasar Rasha tare da karbar sojojin na Rasha bayan ficewar na Faransa da Amurka.

An dai rawaito yadda sojin kasar ta Rasha suka maye gurbin sojin Amurka a sansanin sojin da suka zauna na shekaru da dama.

Ikirari:

Wasu shafukan sada zumunta sun rawaito Firaministan Nijar Ali Lamine Zeine yayi ikirarin cewa babu wani sojan kasar waje a kasar ta Nijar a yanzu haka. Yayi wannan jawabi  ne a birnin Dakar babban birinin kasar Senagal.

Wani shafin Facebook mai suna Nijer 24 ya wallafa wannan ikirari.

Shima wani shafi mai suna Niger 227 post Tv  ya wallafa wannan ikirarin.

Hoton labarin da aka jirkita kuma yake cigaba da yaduwa

Bincike:

Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta gano cewa sojojin kasar Rasha sun sauka kasar Nijar a ranar 4/12/2024 kaamar yadda hukumar tsaro ta Rasha a Africa mai suna The Africa Corps ta wallafa a shafin ta na X(Twitter).

Haka zalika a watan mayun shekarar da ta gabata kafar dillancin labarai ta Reuters ta rawaito cewa sojojin kasar Rasha sun maye gurbin dakarun sojin Amurka a sansanin da suka zauna.

A watan Mayu ne dai kasar ta Nijar ta fice daga yarjejeniyar tattara bayanan tsaro da Rasha da Turkiyya.

Duk da wadannan bayanai dai binciken Alkalanci ya tabbatar da cewa har zuwa watan Oktoba akwai sojojin ƙasar Rasha a ƙasar Nijar, domin an hangesu a bidiyon da kafafen yada labaran kasar suka wallafa na yaye sojoji a Tilliberi da kuma lokacin da shugaban Nijar Tiani ya ziyarci Tilliberi.

Ya zuwa yanzu duk da girman ficewar sojin ƙasashen waje, Nijar da Rasha basu bayyana ficewar dakarun sojin Rasha daga Nijar ba.

Sakamakon bincike:

Bisa kasa samun inda hukumomin Nijar da Rasha suka bayyana ficewar sojin da suka zo Nijar shekarar data gabata suka kuma maye gurbin sansanin sojin Amurka, Sannan ƴan jaridu da mutanen a garin Tilliberi sun tabbatar da ganin sojin Rasha lokacin da shugaban ƙasar Nijar Tiani yakai ziyara. Haka zalika an gano sojin ƙasashen waje a bidiyon taron yaye sojojin ƙasar ta Nijar a satin daya gabata. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin babu sojin ƙasashen waje a Nijar jirkata bayani ne wato misleading a turance.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar