BindiddigiƘarya ne: Ghana bata ce zata dawo da duk...

Ƙarya ne: Ghana bata ce zata dawo da duk ƴan Najeriya ba

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa bayanan shugaban kasar Ghana John Mahama, ministan harkokin wajen Ghana da suka ce ƙasar bata da shirin maida ƴan Najeriya ƙasar su, sannan kuma an kasa samun labarin daga sahihan gidajen jaridu, wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin ƙarya ne.

 

Akwai dai kiraye-kirayen da wasu ƴan ƙasar Ghana keyi na gani gwamnatin ƙasar ta maida ƴan Najeriya ƙasar tun bayan batun naɗin sarautar Sarki ƴan ƙabilar Igbo a ƙasar ta Ghana.
Wasu da dama sun ƴada tsoffin bidiyo, hotuna dama waɗanda aka haɗa ta amfani da ƙirƙirrarriyar basirar AI a matsayin zanga-zangar korar ƴan Najeriya.
Wasu ƴan ƙasar ta Ghana dai sunyi zanga-zangar korar ƴan Najeriya daga ƙasar su a ƙarshen watan Yuli.
Iƙirari:
Wani shafin Tiktok ya wallafa wani bidiyo da aka ga wani na iƙirarin cewa ƙasar Ghana ta amince a mayar da ƴan Najeriya ƙasarsu. ((https://vm.tiktok.com/ZSSa1RsBA/))
“Ghana nan har an zauna an yanke hukuncin babu mafita illa dawo da ƴan Najeriya, domin suka bari hakan ya cigaba da wanzuwa zamu mamaye musu ƙasar su.”
Bincike:
Duk da cewa a shekarun baya Ghana ta taɓa dawo da ƴan Najeriya, to amma wannan sabon kiraye-kirayen bai sanya gwamnatin ƙasar ko majalisar dokokin ƙasar amincewa da dawowa da ƴan Najeriya ba.
Shugaban kasar Ghana John Mahama ya tabbatarwa ‘yan Najeriya mazauna Ghana cewa babu batun maida su gida Najeriya.
Shugaba Mahama ya fadi hakan ne yayin da ya karbi bakuncin tawagar Najeriya bisa jagorancin ministar kasa a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya inda suka je Birnin Accra domin tattaunawa da hukumomin Ghana.
Shugaban Kasar Ghana John Mahama da tawagar Najeriya
A wata ganawa da ministan harkokin wajen Ghana da takwarar sa ministar ƙasa a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya Bianca Ojukwu, gwamnatin Ghana ta tabbatar da cewa bata da shirin kora ko maida ƴan Najeriya.
Alkalanci ta tuntubi wani ɗan jaridar ƙasar Ghana
Kent Mensah inda ya bayyana cewa ƙarya ake yaɗawa kan cewa Ghana ta amince ta kori ƴan Najeriya, ya ƙara da cewa ko kiraye-kiraye da zanga-zangar da akayi mutane ƙalilan ne ke wannan buƙatar.
Haka zalika babu wata sahihiyar kafar yaɗa labarai data ruwaito cewa gwamnantin Ghana ta amince ta dawo da ƴan Najeriya.
Sakamakon bincike:
Bisa bayanan shugaban kasar Ghana John Mahama, ministan harkokin wajen Ghana da suka  ce ƙasar bata da shirin maida ƴan Najeriya ƙasar su, sannan kuma an kasa samun labarin daga sahihan gidajen jaridu, wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin ƙarya ne.
Kamaru ta bada umarnin kama ƴan Najeriya?
A bidiyon da aka wallafa a shafin TIKTOK din ya ƙa ra da cewa ƙasar Kamaru sun daɗe da bada umarnin kama ƴan Najeriya a ƙasar.
“Nan Kamaru tun kimanin shekara guda ma aka sanar da kamen ƴan Najeriya ana dawo dasu ƙasarsu. Kamaru ɗan Najeriya zai shiga ana sarautar da.”
Binciken kafar tantance labarai ta Alkalanci bai gano inda aka ruwaito cewa hukumomin ƙasar Kamaru sun bada umarnin farauta ko kama ƴan Najeriya dake zaune a ƙasar ba.
Ofishin jakadancin Najeriya a Douala Kamaru ya bayyana a shafinsa cewa akwai ƴan Najeriya akalla miliyan bakwai (7miliyan) a ƙasar Kamaru.
Sakamakon bincike:
Bisa rashin samun labarin cewa ƙasar Kamaru ta bada umarnin farautar da kuma kama ƴan Najeriya a ƙasar. Domin kuwa irin wannan labari yayi girman da manyan kafafen yaɗa labarai dole su rawaito kuma zai zama batun diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar