BindiddigiShin Nijar ta rabu da Faransanci?

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

-

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar ta bar harshen Faransanci.
To sai dai  ba kamar yadda wasu suka fahimci labarin ba ga yadda abin yake.
A yanzu dai kasar ta Nijar ta tabbatar da cewa Hausa ta zama harshen ƙasa wato langue nationale a Faransanci.

Wannan na nufin cewa harshen Hausa an amince shi a matsayin harshen da ke da muhimmanci wajen adana al’adu, sadarwa a tsakanin jama’a, da koyar da ilimi a matakin farko wato firamare amma hakan ba yana nufin baza’a koyar da yaren Faransanci ba. Haka zalika kasar ta bayyana wasu yaruka a kasar a matsayin masu muhimmanci.

Amfani da Hausa a matsayin harshen ƙasa yana nufin za a iya amfani da shi a:

Makarantun firamare.

Za’a dinga sadarwa da shirye-shirye a rediyo da Talabijin.

Tattaunawa tsakanin al’umma da hukumomi a matakin ƙasa.

Wayar da kan mutane kan wasu al’amuran da suka shafe su ko suka shafi kasa.

To amma inda gizo ke sakar shine harshen Faransanci har yanzu shine harshen aiki wato langues de travail a Faransanci.

Faransanci shine harshen da gwamnati za ta cigaba da amfani da shi wajen:
To amma fa baya ga Faransanci kasar ta kara da Turancin Ingilishi a matsayin harshen gwamnati.

sune dai za’a dinga;

Rubuce-rubuce a hukumance.

Takardun gwamnati da dokoki.

Tattaunawa da kasashen waje.

Zaman kotu da yanke hukunci a kotu.

Rubutu da karatu a jami’o’i da sauran manyan makarantu.

Kasar ta Nijar dai ba ta cire Faransanci a matsayin yaren gwamnati ba sai dai kara harshen turancin Ingilishi kamar yadda kasar Algeria tayi inda ake koyar da yara yarukan biyu a makarantu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Najeriya-Saudiyya sun karyata labarin cewa za’a hana ‘yan kasar bizar shiga Saudiyya

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta karyata ikirarin karya da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani, wanda ke cewa...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar