BindiddigiWasu labaran ƙarya dake yaduwa kan barazanar Trump ga...

Wasu labaran ƙarya dake yaduwa kan barazanar Trump ga Najeriya

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa kasa samun wadannan a gidajen jaridun ƙasar Nijar da Burkina Faso da kuma bayanin jami'in ma'aikatar harkokin wajen ta Nijar da ya tabbatar wa Alkalanci cewa wannan labari ba gaskiya bane, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin ƙarye ne.
A duk lokacin da aka sami wasu manyan bayanai musamman tsakanin ƙasa da ƙasa ko wasu jigogin siyasa, wasu kan yaɗa labaran ƙarya domin cimma manufa.
Iƙirari:
Akwai wani iƙirari dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta ina ake iƙirarin cewa shugaban Nijar yace ya sha alwashin harbo makamin da Amurka zata harba zuwa Najeriya.
Misali wannan yayi ikirari kamar haka;
“Shugaban mulkin soji na kasar Nijar Janar Muhammad Tchiani ya bayyana cewar ku barta ta harbo, babu wani màkàmìñ daya isa ya gitta ta sararin samaniyar kasar Nijar ba tare da mun kàkkàɓo shi ba, kuma a shirye muke da mu tsunduma cikin yà+ƙì gadan gadan da Amurka matuƙar tayi gigin kaiwa ƴan uwanmu na Najeriya hà+rì.”
Labarin karya dake yaduwa

Shima wannan shafin na Facebook yayi makamancin wancan ikirarin, haka zalika wannan shafin.

Bincike:

Duk da girman wannan bayani dai gidan jaridar ƙasar bai rawaito labari makamancin hakan ba. Haka zalika jami’i a ma’aikatar harkokin wajen Nijar ya faɗawa Alakalanci cewa ya zuwa yanzu babu wani bayani da gwamnatin Nijar ta fitar dangane da abinda ke faruwa tsakanin Nijar da Amurka.

Sakamakon bincike:
Bisa kasa samun wannan labari a gidajen jaridun ƙasar Nijar da kuma bayanin jami’in ma’aikatar harkokin wajen ta Nijar da ya tabbatar wa Alkalanci cewa wannan labari ba gaskiya bane, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin ƙarye ne.
Shugaban Burkina Faso
Iƙirari:
Akwai wasu shafukan da suka yaɗa cewa shugaban Burkina Faso Ibrahim Traore ya gargaɗi Amurka da kada ta kaiwa Najeriya hari.
Wannan  shafin na Facebook har sanya murya yayi a matsayin rahoto tare da yada ikirarin cewa shugaban Burkina Faso yayi magana kan wannan batu na Najeriya da Amurka.
Labarin karya dake yaduwa
Shi kuma wannan shafin na Facebook cewa yayi shugaban na Burkina Faso ya gargadi shugaban Amurka Trump kan Najeriya.
Labarin karya dake yaduwa
Bincike:
Shi ma wannan labarin duk da girman sa babu wata sahihiyar kafar yaɗa labarai data rawaito wannan labari.
Haka zalika Alkalanci ta duba shafin ma’aikatar harkokin wajen Burkina Faso da na gwamnatin ƙasar amma babu makamancin wannan labari.
Sakamakon bincike:
Kasancewar wannan labari ne mai girma wanda kuma kasa ganin shi a sahihan kafafen jaridu na nuna cewa labarai. Yana da alamar tambaya. Bisa kasa samun inda wannan labarin ya fito yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa haɗa shi akai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar