Fayyace abubuwaWaɗanne ƙasashe ne ke rura wutar yaƙin Sudan?

Waɗanne ƙasashe ne ke rura wutar yaƙin Sudan?

-

Yaƙin Sudan dai ana yin sane tsakanin dakarun sojin ƙasar wanda  Janar Abdul Fatah Al-Burhan ke shugabanta kuma shine shugaban ƙasa da dakarun RSF da Janar Mohammed Hamdan Dagalo ke shugabanta.

Su dai dakarun RSF an samar dasu ne a shekarar 2013, wanda à baya suka kasance cikin ƙungiyar janjaweed da sukai yaƙi a yankin Darfur kuma ake zargi da kisan ƙare dangi a shekarar 2003.
Tun daga wancan lokaci dai Janar Dagalo ya samar da dakarun da ake amfani da su wajen yaƙi a ƙasashen Libya da Yemen.
Janar Dagalo ya buƙaci a haɗe dakarun RSF da sojojin ƙasar tare da basu ikon jagorancin soji, haka zalika ya bukaci ya kasance mai kula da ma’adanin zinaren ƙasar.
Ƙasashen Amurka, Burtaniya, Majalisar Dinkin Duniya da Ƙungiyar human rights watch sun zargi RSF da kisan ƙabilanci wato kashe ƙabilun da ba larabawa ba, da baƙaƙen fata.
Duk da cewa ƙungiyoyi irin su Amnesty sun koka kan yadda ƙasashen duniya sukai shakulatin ɓangaro da yaƙin Sudan, to amma shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron a bara ya ayyana taimakon Euro biliyan biyu domin tallafawa waɗanda wannan yaƙi ya shafa a Sudan.

Ƙasashen dake rura wutar yaƙin:

 ƙasashen Libya, Chad da Sudan ta Kudu ne dai wani jami’in majalissar ɗinkin duniya ke zargi a matsayin masu rura wutar tun farkon yaƙin har zuwa yanzu, a cewar jaridar dillancin labarai ta Reuters.
Ƙasashen Burtaniya da Amurka kuwa sun zargi kasar haɗaɗɗiyar daular Larabawa UAE da cewa itace ke baiwa RSF makamai, wanda ƙasar ta musanta.
Har ila yau ana zargin ƙasar Saudiyya da hannu wajen goyon bayan RSF kasancewar dakarun RSF ne ƙasar ta Saudiyya ke amfani wajen yaƙi a ƙasar Yemen.
A baya-bayan nan kuma an gano ƙasar Kenya wanda shugaban ƙasar ya karbi tare da amincewa da dakarun RSF wajen kafa shugabanci a ƙasar Sudan wanda ƙasashen duniya da dama sukai Allah wadai da matakin na Kenya.
Wani ɗan jaridar ƙasar Kenya ya bayyanawa Alkalanci cewa dalilin da yasa shugaban Kenya Ruto ke goyon bayan mayaƙan RSF shine shugabannin mayaƙan abokan kasuwancin sa ne da daɗewa.
A ƴan kwanakin da suka gabata ne dai dakarun sojin ƙasar ta Sudan suka kwace fadar shugaban kasa da babban birnin ƙasar Khartoum daga hannun RSF.
Labarai Masu Alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar