BindiddigiShin Nijar Zata Gina Katanga Tsakaninta Da Najeriya?

Shin Nijar Zata Gina Katanga Tsakaninta Da Najeriya?

-

Akwai dai zarge-zarge tsakanin gwamnatin Najeriya da Nijar tun bayan juyin mulki da sojoji sukayi a kasar, wanda ke rura wutar labaran karya dangane da kasashen biyu.

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani ikirari (archived here) a ranar lahadi 22/12/2024 inda ya rubuta cewa “ 🛑Nijar zata gina katanga mai tsawon Km 1497 a iyaka tsakaninta da Nigeria domin karfafa tsaro a kasar.”
W annan wallafa dai ta sami tofa albarkacin baki sama da dari uku kasa da mintuna talatin da wallafawa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Nijar Amadou Ango Souley ((Responsable de la communication du Ministère des Affaires Étrangères auprès du Ministre)) data tambayeshi cewa baya ga zarge-zargen da sukewa gwamnatin Najeriya akwai shirin gina katanga tsakanin Nijar da Najeriya? Sai yayi dariya yace “wannan magana ce kawai babu wani shiri irin wannan, shirmen ‘yan kafafen sada zumunta ne kawai.”

Sakamakon Bincike:

Bisa bayanan mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje ta Nijar din na cewa babu wani shiri makamancin haka yasa kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar