BindiddigiShin Nijar Zata Gina Katanga Tsakaninta Da Najeriya?

Shin Nijar Zata Gina Katanga Tsakaninta Da Najeriya?

-

Akwai dai zarge-zarge tsakanin gwamnatin Najeriya da Nijar tun bayan juyin mulki da sojoji sukayi a kasar, wanda ke rura wutar labaran karya dangane da kasashen biyu.

Batu:

Akwai wani shafin Facebook mai suna Damagaram Post ya wallafa wani ikirari (archived here) a ranar lahadi 22/12/2024 inda ya rubuta cewa “ 🛑Nijar zata gina katanga mai tsawon Km 1497 a iyaka tsakaninta da Nigeria domin karfafa tsaro a kasar.”
W annan wallafa dai ta sami tofa albarkacin baki sama da dari uku kasa da mintuna talatin da wallafawa.

Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Nijar Amadou Ango Souley ((Responsable de la communication du Ministère des Affaires Étrangères auprès du Ministre)) data tambayeshi cewa baya ga zarge-zargen da sukewa gwamnatin Najeriya akwai shirin gina katanga tsakanin Nijar da Najeriya? Sai yayi dariya yace “wannan magana ce kawai babu wani shiri irin wannan, shirmen ‘yan kafafen sada zumunta ne kawai.”

Sakamakon Bincike:

Bisa bayanan mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje ta Nijar din na cewa babu wani shiri makamancin haka yasa kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar